< Hebræerne 1 >
1 Efter at Gud fordum havde talt mange Gange og på mange Måder, til Fædrene ved Profeterne,
A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
2 så har han ved Slutningen af disse Dage talt til os ved sin Søn, hvem han har sat til Arving af alle Ting, ved hvem han også har skabt Verden; (aiōn )
amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
3 han, som - efterdi han er hans Herligheds Glans og hans Væsens udtrykte Billede og bærer alle Ting med sin Krafts Ord - efter at have gjort Renselse fra Synderne har sat sig ved Majestætens højre Hånd i det høje,
Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
4 idet han er bleven så meget ypperligere end Englene, som han har arvet et herligere Navn fremfor dem.
Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
5 Thi til hvilken af Englene sagde han nogen Sinde: "Du er min Søn, jeg har født dig i Dag"? og fremdeles: "Jeg skal være ham en Fader, og han skal være mig en Søn"?
Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
6 Og når han atter indfører den førstefødte i Verden, hedder det: "Og alle Guds Engle skulle tilbede ham".
Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
7 Og om Englene hedder det: "Han gør sine Engle til Vinde og sine Tjenere til Ildslue";
Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
8 men om Sønnen: "Din Trone, o Gud! står i al Evighed, og Rettens Kongestav er dit Riges Kongestav. (aiōn )
Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
9 Du elskede Retfærdighed og hadede Lovløshed, derfor har Gud, din Gud, salvet dig med Glædens Olie fremfor dine Medbrødre".
Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
10 Og: "Du, Herre! har i Begyndelsen grundfæstet Jorden, og Himlene ere dine Hænders Gerninger.
Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
11 De skulle forgå, men du bliver; og de skulle til Hobe ældes som et Klædebon,
Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
12 ja, som et Klæde skal du sammenrulle dem, og de skulle omskiftes; men du er den samme, og dine År skulle ikke få Ende".
Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
13 Men til hvilken af Englene sagde han nogen Sinde: "Sæt dig ved min højre Hånd, indtil jeg får lagt dine Fjender som en Skammel for dine Fødder"?
Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
14 Ere de ikke alle tjenende Ånder, som udsendes til Hjælp for deres Skyld, der skulle arve Frelse?
Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?