< Hebræerne 3 >

1 Derfor, hellige Brødre, delagtige i en himmelsk Kaldelse! ser hen til vor Bekendelses Udsending og Ypperstepræst, Jesus,
Don haka yanuwana tsarkaka, a bokan kira a samaniya. Yi la'akari da Yesu. wato Manzo da babban firist na shaidar bangaskiyarmu.
2 der var tro imod den, som beskikkede ham, ligesom også Moses var det i hele hans Hus.
Shi amintacce ne na Allah, wanda ya bashi hidima, kamar yadda Musa ya kasance amintacce a gidan Allah.
3 Thi han er kendt værdig til større Herlighed end Moses, i samme Mål som den, der har indrettet et Hus, har større Ære end Huset selv.
Gama Yesu ya cancanci daukaka mafi girma fiye da ta Musa. Domin wanda ya gina gida, ya fi gidan nan daukaka.
4 Thi hvert Hus indrettes af nogen; men den, som har indrettet alt, er Gud.
Gama kowane gida, akwai wanda ya gina shi, amma mai ginin komai shine Allah.
5 Og Moses var vel tro i hele hans Hus, som en Tjener, til Vidnesbyrd om, hvad der skulde tales;
Musa hakika amintaccen bawa ne a gidan Allah, yana ba da shaidar abubuwan da za su faru a nan gaba.
6 men Kristus er det som en Søn over hans Hus; og hans Hus ere vi, såfremt vi fastholde Håbets Frimodighed og Ros urokket indtil Enden.
Amma Almasihu shi Da ne mai mulki a gidan Allah. Mu ne gidansa idan mun rike begenmu da dukkan zuciyarmu.
7 Derfor, som den Helligånd siger: "I Dag, når I høre hans Røst,
Saboda haka, kamar yadda Ruhu Mai Tsarki ya fadi: ''Yau, Idan kun ji muryarsa,
8 da forhærder ikke eders Hjerter, som det skete i Forbitrelsen, på Fristelsens Dag i Ørkenen,
kada ku taurare zuciyarku kamar yadda 'ya'yan isra'ila suka yi cikin tawaye a lokacin gwaji a jeji.
9 hvor eders Fædre fristede mig ved at sætte mig på Prøve, og de så dog mine Gerninger i fyrretyve År.
A lokacin nan ne kakanninku suka yi mani tawaye, ta wurin gwada ni, bayan shekara arba'in suna ganin ayyukana.
10 Derfor harmedes jeg på denne Slægt og sagde: De fare altid vild i Hjertet; men de kendte ikke mine Veje,
Saboda haka na yi bakin ciki da wannan tsarar, sai na ce,' Kullum suna yawan bijirewa a zukatansu. Basu san tafarkuna ba.'
11 så jeg svor i min Vrede: Sandelig, de skulle ikke gå ind til min Hvile" -
Don haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ba za su shiga cikin hutuna ba.”
12 så ser til, Brødre! at der ikke nogen Sinde i nogen af eder skal findes et ondt, vantro Hjerte, så at han falder fra den levende Gud.
Ku yi hankali 'yan'uwa kada a tarar da mummunar zuciya marar bangaskiya a tsakaninku, zuciya wadda ke juyawa daga Allah mai rai.
13 Men formaner hverandre hver Dag, så længe det hedder "i Dag", for at ikke nogen af eder skal forhærdes ved Syndens Bedrag.
Maimakon haka, ku karfafa juna a kowacce rana, muddun muna cikin wannan rana kada wani cikinku ya taurare zuciyarsa saboda yaudarar zunubi.
14 Thi vi ere blevne delagtige i Kristus, såfremt vi fastholde vor første Fortrøstning urokket indtil Enden.
Gama mun zama abokan aiki da Almasihu, idan mun rike begenmu cikinsa da karfi, daga farko zuwa karshe.
15 Når der sigs: "I Dag, - når I høre hans Røst, da forhærder ikke eders Hjerter som i Forbitrelsen":
Game da wannan, an fadi “Yau idan kun saurari muryarsa, kada ku taurare zuciyarku, kamar a kwanakin tawaye nan.”
16 hvem vare da vel de, som hørte og dog voldte Forbitrelse? Mon ikke alle, som gik ud af Ægypten ved Moses?
Su wanene suka ji muryar Allah suka yi tawaye? Ba wadanda Musa ya yi masu jagora daga Masar ba ne?
17 Men på hvem harmedes han i fyrretyve År? Mon ikke på dem, som syndede, hvis døde Kroppe faldt i Ørkenen?
Kuma da su wa Allah ya yi fushi shekara arba'in? Ba da wadanda suka yi zunubi ba ne, wadanda gawawwakinsu suka warwatsu a jeji?
18 Og over for hvem tilsvor han, at de ikke skulde gå ind til hans Hvile, uden dem, som vare blevne genstridige?
Da su wa Allah ya rantse ba za su shiga hutunsa ba? In ba wadanda suka yi masa rashin biyayya ba?
19 Og vi se, at de ikke kunde gå ind på Grund af Vantro.
Mun kuma gani cewa basu iya shiga hutunsa ba saboda rashin bangaskiyarsu.

< Hebræerne 3 >