< Hebræerne 3 >

1 Derfor, hellige Brødre, delagtige i en himmelsk Kaldelse! ser hen til vor Bekendelses Udsending og Ypperstepræst, Jesus,
Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
2 der var tro imod den, som beskikkede ham, ligesom også Moses var det i hele hans Hus.
Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
3 Thi han er kendt værdig til større Herlighed end Moses, i samme Mål som den, der har indrettet et Hus, har større Ære end Huset selv.
An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
4 Thi hvert Hus indrettes af nogen; men den, som har indrettet alt, er Gud.
Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
5 Og Moses var vel tro i hele hans Hus, som en Tjener, til Vidnesbyrd om, hvad der skulde tales;
Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
6 men Kristus er det som en Søn over hans Hus; og hans Hus ere vi, såfremt vi fastholde Håbets Frimodighed og Ros urokket indtil Enden.
Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
7 Derfor, som den Helligånd siger: "I Dag, når I høre hans Røst,
Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
8 da forhærder ikke eders Hjerter, som det skete i Forbitrelsen, på Fristelsens Dag i Ørkenen,
kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
9 hvor eders Fædre fristede mig ved at sætte mig på Prøve, og de så dog mine Gerninger i fyrretyve År.
inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
10 Derfor harmedes jeg på denne Slægt og sagde: De fare altid vild i Hjertet; men de kendte ikke mine Veje,
Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
11 så jeg svor i min Vrede: Sandelig, de skulle ikke gå ind til min Hvile" -
Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
12 så ser til, Brødre! at der ikke nogen Sinde i nogen af eder skal findes et ondt, vantro Hjerte, så at han falder fra den levende Gud.
Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
13 Men formaner hverandre hver Dag, så længe det hedder "i Dag", for at ikke nogen af eder skal forhærdes ved Syndens Bedrag.
Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
14 Thi vi ere blevne delagtige i Kristus, såfremt vi fastholde vor første Fortrøstning urokket indtil Enden.
Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
15 Når der sigs: "I Dag, - når I høre hans Røst, da forhærder ikke eders Hjerter som i Forbitrelsen":
Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
16 hvem vare da vel de, som hørte og dog voldte Forbitrelse? Mon ikke alle, som gik ud af Ægypten ved Moses?
Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
17 Men på hvem harmedes han i fyrretyve År? Mon ikke på dem, som syndede, hvis døde Kroppe faldt i Ørkenen?
Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
18 Og over for hvem tilsvor han, at de ikke skulde gå ind til hans Hvile, uden dem, som vare blevne genstridige?
Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
19 Og vi se, at de ikke kunde gå ind på Grund af Vantro.
Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.

< Hebræerne 3 >