< 1 Mosebog 7 >

1 Derpå sagde HERREN til Noa: Gå ind i Arken med hele dit Hus, thi dig har jeg fundet retfærdig for mine Øjne i denne Slægt.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 Af alle rene Dyr skal du tage syv Par, Han og Hun, og af alle urene Dyr eet Par, Han og Hun,
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 ligeledes af Himmelens Fugle syv Par, Han og Hun, for at de kan forplante sig på hele Jorden.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 Thi om syv Dage vil jeg lade det regne på Jorden i fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter og udslette alle Væsener, som jeg har gjort, fra Jordens Flade."
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Og Noa gjorde ganske som HERREN havde pålagt ham.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 Noa var 600 År gammel, da Vandfloden kom over Jorden.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 Noa gik med sine Sønner, sin Hustru og sine Sønnekoner ind i Arken for at undslippe Flodens Vande.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 De rene og de urene Dyr, Fuglene og alt, hvad der kryber på Jorden,
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 gik Par for Par ind i Arken til Noa, Han og Hundyr, som Gud havde pålagt Noa.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 Da nu syv Dage var omme, kom Flodens Vande over Jorden;
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 i Noas 600de Leveår på den syttende Dag i den anden Måned, den Dag brast det store Verdensdybs Kilder, og Himmelens Sluser åbnedes,
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 og Regnen faldt over Jorden i fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 Selvsamme Dag gik Noa ind i Arken og med ham hans Sønner Sem, Kam og Jafet, hans Hustru og hans tre Sønnekoner
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 og desuden alle vildtlevende Dyr efter deres Arter, alt Kvæg efter dets Arter, alt Kryb på Jorden efter dets Arter og alle Fugle efter deres Arter, alle Fugle, alt, hvad der har Vinger;
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 af alt Kød, som har Livsånde, gik Par for Par ind i Arken til Noa;
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 Han og Hundyr af alt Kød gik ind, som Gud havde påbudt, og HERREN lukkede efter ham.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 Da kom Vandfloden over Jorden i fyrretyve Dage, og Vandet steg og løftede Arken, så den hævedes over Jorden.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 Og Vandet steg og stod højt over Jorden, og Arken flød på Vandet;
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 og Vandet steg og steg over Jorden, så de højeste Bjerge under Himmelen stod under Vand;
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 femten Alen stod Vandet over dem, så Bjergene stod helt under Vand.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 Da omkom alt Kød, som rørte sig på Jorden, Fugle, Kvæg, vildtlevende Dyr og alt Kryb på Jorden og alle Mennesker;
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 alt, i hvis Næse det var Livets Ånde, alt, hvad der var på det faste Land, døde.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 Således udslettedes alle Væsener, der var på Jordens Flade, Mennesker, Kvæg, Kryb og Himmelens Fugle; de udslettedes af Jorden, og tilbage blev kun Noa og de, der var hos ham i Arken.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 Vandet steg over Jorden i 150 Dage.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.

< 1 Mosebog 7 >

The Great Flood
The Great Flood