< 1 Mosebog 40 >

1 Nogen Tid efter hændte det, at Ægypterkongens Mundskænk og Bager forbrød sig mod deres Herre Ægypterkongen,
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 og Farao vrededes på sine to Hofmænd, Overmundskænken og Overbageren,
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 og lod dem sætte i Forvaring i Livvagtens Øverstes Hus, i samme Fængsel, hvor Josef sad fængslet;
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 og Livvagtens Øverste gav dem Josef til Opvartning, og han gik dem til Hånde. Da de nu havde været i Forvaring en Tid lang,
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 drømte Ægypterkongens Mundskænk og Bager, som sad i Fængselet, samme Nat hver sin Drøm med sin særlige Betydning.
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 Da Josef om Morgenen kom ind til Faraos Hofmænd, der sammen med ham var i Forvaring i hans Herres Hus, og så, at de var nedslåede,
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 spurgte han dem: "Hvorfor ser I så ulykkelige ud i Dag?"
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 Besvarede: "Vi har haft en Drøm, og her er ingen, som kan tyde den." Da sagde Josef til dem: "Er det ikke Guds Sag at tyde Drømme? Fortæl mig det da!"
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 Så fortalte Overmundskænken Josef sin Drøm og sagde: "Jeg så i Drømme en Vinstok for mig;
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 på Vinstokken var der tre Ranker, og næppe havde den sat Skud. før Blomsterne sprang ud, og Klaserne bar modne Druer;
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 og jeg havde Faraos Bæger i Hånden og tog Druerne og pressede dem i Faraos Bæger og rakte Farao det."
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 Da sagde Josef: "Det skal udtydes således: De tre Ranker betyder tre Dage;
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 om tre Dage skal Farao løfte dit Hoved og genindsætte dig i dit Embede, så du atter rækker Farao Bægeret som før, da du var hans Mundskænk.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Vilde du nu blot tænke på mig, når det går dig vel, og vise mig Godhed og omtale mig for Farao og således hjælpe mig ud af dette Hus;
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 thi jeg er stjålet fra Hebræernes Land og har heller ikke her gjort noget, de kunde sætte mig i Fængsel for."
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 Da nu Overbageren så, at Josef gav Mundskænken en gunstig Tydning, sagde han til ham: "Jeg havde en lignende Drøm: Se, jeg bar tre Kurve Hvedebrød på mit Hoved.
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 I den øverste Kurv var der alle Hånde Bagværk til Faraos Bord, men Fuglene åd det af Kurven på mit Hoved!"
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 Da sagde Josef: "Det skal udtydes således: De tre Kurve betyder tre Dage;
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 om tre Dage skal Farao løfte dit Hoved og hænge dig op på en Pæl, og Fuglene skal æde Kødet af din Krop!"
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 Tre Dage efter, da det var Faraos Fødselsdag, gjorde han et Gæstebud for alle sine Tjenere, og da løftede han Overmundskænkens og Overbagerens, Hoveder iblandt sine Tjenere.
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 Overmundskænken genindsatte han i hans Embede, så han atter rakte Farao Bægeret,
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
22 og Overbageren lod han hænge, som Josef havde tydet det for dem.
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 Men Overmundskænken tænkte ikke på Josef; han glemte ham.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.

< 1 Mosebog 40 >