< 1 Mosebog 15 >

1 Nogen Tid efter kom HERRENS Ord til Abram i et Syn således: "Frygt ikke, Abram, jeg er dit Skjold; din Løn skal blive såre stor!"
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
2 Men Abram svarede: "Herre", HERRE, hvad kan du give mig, når jeg dog går barnløs bort, og en Mand fra Damaskus, Eliezer, skal arve mit Hus."
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
3 Og Abram sagde: "Du har jo intet Afkom givet mig, og se, min Hustræl kommer til at arve mig!"
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
4 Og se, HERRENs Ord kom til ham således: "Han kommer ikke til at arve dig, men den, der udgår af dit Liv, han skal arve dig."
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
5 Derpå førte han ham ud i det fri og sagde: "Se op mod Himmelen og prøv, om du kan tælle Stjernerne!" Og han sagde til ham: "Således skal dit Afkom blive!"
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
6 Da troede Abram HERREN, og han regnede ham det til Retfærdighed.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
7 Derpå sagde han til ham: "Jeg er HERREN, som førte dig bort fra Ur Kasdim for at give dig dette Land i Eje!"
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
8 Men han svarede: "Herre, HERRE, hvorpå kan jeg kende, at jeg skal få det i Eje?"
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
9 Da sagde han til ham: "Tag mig en treårs Kvie, en treårs Ged og en treårs Væder, en Turteldue og en Småfugl!"
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
10 Så tog han alle disse Dyr skar dem midt over og lagde Halvdelene over for hinanden; dog skar han ikke Fuglene over.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
11 Da slog der Rovfugle ned på de døde Kroppe, men Abram skræmmede dem bort.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
12 Da Solen så var ved at gå ned, faldt der Dvale over Abram, og se, Rædsel faldt over ham, et stort Mørke.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
13 Og han sagde til Abram: "Vide skal du, at dit Afkom skal bo som fremmede i et Land, der ikke er deres eget; de skal trælle for dem og mishandles af dem i 400 År.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
14 Dog vil jeg også dømme det Folk, de kommer til at trælle for, og siden skal de vandre ud med meget Gods.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
15 Men du skal fare til dine Fædre i Fred og blive jordet i en god Alderdom.
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
16 I fjerde Slægtled skal de vende tilbage hertil; thi endnu er Amoriternes Syndeskyld ikke fuldmoden."
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
17 Da Solen var gået ned og Mørket faldet på, viste der sig en rygende Ovn med en flammende Ildslue, der skred frem mellem de sønderskårne Kroppe.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
18 På den Dag sluttede HERREN Pagt med Abram, idet han sagde: "Dit Afkom giver jeg dette Land fra Ægyptens Bæk til den store Flod, Eufratfloden,
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
19 det er Keniterne, Henizziterne, Kadmoniterne,
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
20 Hetiterne, Perizziterne, Refaiterne,
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
21 Amoriterne, Kana'anæerne, Girgasjiterne, Hivviterne og Jebusiterne."
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”

< 1 Mosebog 15 >