< Ezekiel 37 >

1 Herrens hånd kom over mig, og han førte mig i ånden ud og satte mig midt i dalen. Den var fuld af Ben;
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 og han førte mig rundt omkring dem, og se, de lå i store Mængder ud over Dalen, og se, de var aldeles tørre.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 Derpå sagde han til mig: "Menneskesøn! kan disse Ben blive levende?" Jeg svarede: "Herre, HERRE, du ved det!"
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 Så sagde han til mig: Profeter over disse Ben og sig til dem: I tørre Ben, hør HERRENs Ord!
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Så siger den Herre HERREN til disse Ben: Se, jeg bringer Ånd i eder, så I bliver levende.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 Jeg lægger Sener om eder, lader Kød vokse frem på eder, overtrækker eder med Hud og indgiver eder Ånd, så I bliver levende; og I skal kende, at jeg er HERREN.
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 Så profeterede jeg, som mig var pålagt, og der hørtes en Lyd, da jeg profeterede, og se, der hørtes Raslen, og Benene nærmede sig hverandre.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 Og jeg skuede, og se, der kom Sener på dem, Kød voksede frem, og de blev overtrukket med Hud, men der var ingen Ånd i dem.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 Så sagde han til mig: Profeter og tal til Ånden, profeter, du Menneskesøn, og sig til dem: Så siger den Herre HERREN: Ånd, kom fra de fre Verdenshjørner og blæs på disse dræbte, at de må blive levende!
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 Da profeterede jeg, som han bød mig, og Ånden kom i dem, og de blev levende og rejste sig på deres Fødder, en såre, såre stor Hær.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 Derpå sagde han til mig: Menneskesøn! Disse Ben er alt Israels Hus. Se, de siger: "Vore Ben er tørre, vort Håb er svundet, det er ude med os!"
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Profeter derfor og sig til dem: Så siger den Herre HERREN: Se, jeg åbner eders Grave og fører eder ud af dem, mit Folk, og bringer eder til Israels Land;
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 og I skal kende, at jeg er HERREN, når jeg åbner eders Grave og fører eder ud af dem, mit Folk.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 Jeg indgiver eder min Ånd, så I bliver levende, og jeg bosætter eder i eders Land; og I skal kende, at jeg er HERREN; jeg har talet, og jeg fuldbyrder det, lyder det fra HERREN.
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 HERRENs Ord kom til mig således:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 Du, Menneskesøn, tag dig et Stykke Træ og skriv derpå: Juda og hans Medbrødre blandt Israeliterne! Tag så et andet Stykke Træ og skriv derpå: Josef Efraims Træ og hans Medbrødre, alt Israels Hus!
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 Føj dem så sammen til eet Stykke, så de bliver eet i din Hånd.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 Og når så dine Landsmænd siger til dig: "Vil du ikke sige os, hvad du mener dermed?"
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 sig så til dem: Så siger den Herre HERREN: Se, jeg tager Josefs Træ", som var i Efraims Hånd, og Israels Stammer, hans Medbrødre, og føjer dem til Judas Træ og gør dem til eet Stykke og de skal blive eet i Judas Hånd.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 Og Træstykkerne, du skrev på, skal være i din Hånd, så de kan se dem.
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 Tal så til dem: Så siger den Herre HERREN: Se, jeg henter Israeliterne fra Folkene, til hvilke de vandrede hen, og samler dem alle Vegne fra og bringer dem til deres Land.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 Jeg gør dem til eet Folk i Landet på Israels Bjerge; og de skal alle have en og samme Konge og ikke mere være to Folk eller delt i to Riger.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 De skal ikke mere gøre sig urene ved deres Afgudsbilleder og væmmelige Guder eller alle deres Overtrædelser, og jeg vil frelse dem fra alt deres Frafald, hvormed de forsyndede sig, og rense dem, og de skal være mit Folk, og jeg vil være deres Gud.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 Min Tjener David skal være Konge over dem, og alle skal de have en og samme Hyrde. De skal følge mine Lovbud og holde mine Vedtægter og gøre efter dem.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 De skal bo i det Land, jeg gav min Tjener Jakob, der hvor deres Fædre boede; de skal bo der til evig Tid, de, deres Børn og Børnebørn; og min Tjener David skal være deres Fyrste evindelig.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 Jeg slutter en Fredspagt med dem, en evig Pagt skal det være; og jeg gør dem mangfoldige og sætter min Helligdom i deres Midte evindelig;
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 min Bolig skal være over dem; jeg vil være deres Gud, og de skal være mit Folk.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 Og Folkene skal kende, at jeg er HERREN, som helliger Israel, når min Helligdom bliver i deres Midte evindelig
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”

< Ezekiel 37 >