< Ezekiel 35 >

1 HERRENs Ord kom til mig således:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Menneskesøn, vend dit Ansigt mod Seirs Bjergland og profeter imod det
“Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
3 og sig til det: Så siger den Herre HERREN: Se, jeg kommer over dig, Seirs Bjergland, og løfter min Hånd imod dig; jeg gør dig til Ørk og Ødemark,
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
4 dine Byer lægger jeg i Grus. Du selv skal blive til Ørk og kende, at jeg er HERREN.
Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
5 Fordi du nærede evigt Had og i Nødens Stund overgav Israeliterne til Sværdet, da deres Misgerning var fuldmoden,
“‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
6 derfor, så sandt jeg lever, lyder det fra den Herre HERREN: Jeg gør dig til Blod, og Blod skal forfølge dig; sandelig, du forbrød dig ved Blod, og Blod skal forfølge dig.
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
7 Jeg gør Seirs Bjergland til Ørk og Ødemark og udrydder deraf enhver, som kommer og går;
Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
8 jeg fylder dets Bjerge med dræbte; på dine Høje og i dine Dale og Kløfter skal de sværdslagne falde.
Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
9 Jeg gør dig til Ørk for evigt, dine Byer skal ikke bebos; og du skal kende, at jeg er HERREN.
Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
10 Fordi du sagde: "De tvende Folk og de tvende Lande skal tilhøre mig, jeg vil tage dem i Eje!" skønt HERREN var der,
“‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
11 derfor, så sandt jeg lever, lyder det fra den Herre HERREN: Jeg vil gøre med dig efter den Vrede og det Nid, du hadefuldt udviste imod dem, og jeg vil give mig til Hende for dig, når jeg dømmer dig;
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
12 og du skal kende, at jeg er HERREN. Jeg har hørt al den Spot, du udslyngede mod Israels Bjerge: "De er ødelagt, os er de givet til Føde!"
Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
13 Du gjorde dig stor imod mig med din Mund og overfusede mig med Ord; jeg hørte det.
Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
14 Så siger den Herre HERREN: Som det var din Glæde, at mit Land blev Ørk, således vil jeg gøre med dig;
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
15 som det var din Glæde, at Israels Huss Arvelod blev Ørk, således vil jeg gøre med dig. Ørk skal du blive, Seirs Bjergland og hele Edom med; og de skal kende, at jeg er HERREN.
Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”

< Ezekiel 35 >