< Ezekiel 3 >

1 Så sagde han til mig: "Menneskesøn, slug hvad du her har for dig, slug denne Bogrulle og gå så hen og tal til Israels Hus!"
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
2 Så åbnede jeg Munden, og han lod mig sluge Bogrullen
Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
3 og sagde til mig: "Menneskesøn! Lad din Bug fortære den Bogrulle, jeg her giver dig, og fyld dine Indvolde dermed!" Og jeg slugte den, og den var sød som Honning i min Mund.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
4 Så sagde han til mig: "Menneskesøn, gå til Israels Hus og tal mine Ord til dem!
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
5 Thi du sendes til Israels Folk, ikke til et Folk med dybt Mål og tungt Mæle,
Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
6 ikke til mange Hånde Folkeslag med dybt Mål og tungt Mæle, hvis Tale du ikke fatter, hvis jeg sendte dig til dem, vilde de høre dig.
ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
7 Men Israels Hus vil ikke høre dig, thi de vil ikke høre mig; thi hele Israels Hus har hårde Pander og stive Hjerter.
Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
8 Se, jeg gør dit Ansigt hårdt som deres Ansigter og din Pande hård som deres Pander;
Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
9 som Diamant, hårdere end Flint gør jeg din Pande. Frygt ikke for dem og vær ikke ræd for deres Ansigter, thi de er en genstridig Slægt!"
Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
10 Videre sagde han til mig: "Menneskesøn, alle mine Ord, som jeg taler til dig, skal du optage i dit Hjerte og høre med dine Ører;
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
11 og gå så hen til dine landflygtige Landsmænd og tal til dem og sig: Så siger den Herre HERREN! - hvad enten de så hører eller ej!"
Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
12 Så løftede Ånden mig, og jeg hørte bag mig Larmen af et vældigt Jordskælv, da HERRENs Herlighed hævede sig fra sit Sted,
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
13 og Suset af de levende Væseners Vinger, der rørte hverandre, og samtidig Lyden af Hjulene og Larmen af Jordskælvet.
Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
14 Og Ånden løftede mig og førte mig bort, og jeg vandrede bitter og gram i Hu, idet HERRENs Hånd var over mig med Vælde.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
15 Så kom jeg til de landflygtige i Tel-Abib, de, som boede ved Floden Kebar, og der sad jeg syv Dage iblandt dem og stirrede hen for mig.
Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
16 Syv Dage senere kom HERRENs Ord til mig således:
A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
17 Menneskesøn! Jeg sætter dig til Vægter for Israels Hus; hører du et Ord af min Mund, skal du advare dem fra mig.
“Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
18 Når jeg siger til den gudløse: "Du skal visselig dø!" og du ikke advarer ham eller for at bevare hans Liv taler til ham om at omvende sig fra sin gudløse Vej, så skal samme gudløse dø for sin Misgerning, men hans Blod vil jeg kræve af din Hånd.
In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
19 Advarer du derimod den gudløse, og han ikke omvender sig fra sin Gudløshed og sin Vej, så skal samme gudløse dø for sin Misgerning, men du har reddet din Sjæl.
Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
20 Og når en retfærdig vender sig fra sin Retfærdighed og gør Uret, og jeg lægger Anstød for ham, så han dør, og du ikke har advaret ham, så dør han for sin Synd, og den Retfærdighed, han har øvet, skal ikke tilregnes ham, men hans Blod vil jeg kræve af din Hånd.
“Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
21 Har du derimod advaret den retfærdige mod at synde, og han ikke synder, så skal samme retfærdige leve, fordi han lod sig advare, og du har reddet din Sjæl.
Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
22 Siden kom HERRENs Hånd over mig der, og han sagde til mig: "Stå op og gå ud i dalen, der vil jeg tale med dig!"
Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
23 Så stod jeg op og gik ud i Dalen, og se, der stod HERRENs Herlighed, som jeg havde set denved Floden Kebar. Da faldt jeg på mit Ansigt.
Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
24 Men Ånden kom i mig og rejste mig på mine Fødder. Så taIede han til mig og sagde: Gå hjem og luk dig inde i dit Hus!
Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
25 Og du, Menneskesøn, se, man skal lægge Bånd på dig og binde dig, så du ikke kan gå ud iblandt dem;
Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
26 og din Tunge lader jeg hænge ved Ganen, så du bliver stum og ikke kan være dem en Revser; thi de er en genstridig Slægt.
Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
27 Men når jeg taler til dig, vil jeg åbne din Mund, og du skal sige til dem: Så siger den Herre HERREN! Så får den, der vil høre, høre, og den, der ikke vil, får lade være; thi de er en genstridig Slægt.
Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.

< Ezekiel 3 >