< Ezekiel 17 >
1 HERRENs Ord kom til mig således:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Menneskesøn, fremsæt en Gåde og tal i Lignelse til Israels Slægt;
“Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
3 sig: Så siger den Herre HERREN: Den store Ørn med vældigt Vingefang, lange Vinger, tæt Fjederham og brogede Farver kom til Libanon og tog Cederens Top;
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
4 Spidsen af dens Skud brød den af, bragte den til et Kræmmerland og satte den i en Handelsby.
ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
5 Så tog den en Plante der i Landet og plantede den i en Sædemark ved rigeligt Vand...",
“‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
6 for at den skulde vokse og blive en yppig, lavstammet Vinstok, hvis Ranker skulde vende sig til den, og hvis Rødder skulde blive under den. Og den blev en Vinstok, som skød Grene og bredte sine Kviste.
ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
7 Men der var en anden stor Ørn med vældigt Vingefang og rig Fjederham; og se, Vinstokken bøjede sine Rødder imod den og strakte sine Ranker hen til den, for at den skulde give den mere Vand end Bedet, den stod i.
“‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
8 På en frugtbar Mark ved rigeligt Vand var den plantet for at skyde Grene, bære Frugt og blive en herlig Vinstok.
An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
9 Sig derfor: Så siger den Herre HERREN: Mon det lykkes den? Mon den første Ørn ikke rykker dens Rødder op og afriver dens Frugt, så alle de friske Skud tørres hen? Der skal jo ingen kraftig Arm eller mange Folk til at rive den løs fra Roden.
“Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
10 Se, den er plantet, men mon det lykkes den? Mon den ikke, så snart Østenvinden når den, hentørres i Bedet, den voksede i?
Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
11 Og HERRENs Ord kom til mig således:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 Sig til den genstridige Slægt: Ved I ikke, hvad dette betyder? Sig: Babels Konge kom til Jerusalem, tog Kongen og Fyrsterne og førte dem med hjem til Babel.
“Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
13 Derpå tog han entling af kongehuset og sluttede Pagt med ham og lod ham aflægge Ed. Landets Stormænd tog han dog med,
Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
14 for at Riget skulde holdes nede og ikke hovmode sig, men holde hans Pagt, at den måtte stå fast.
don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
15 Men han faldt fra og sendte sine Bud til Ægypten, for at de skulde give ham Heste og Folk i Mængde. Mon det lykkes ham? Mon den, der bærer sig således ad, slipper godt derfra? Skal den, der bryder en Pagt, slippe fra det?
Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
16 Så sandt jeg lever, lyder det fra den Herre HERREN: Hvor den Konge bor, som gjorde ham til Konge, hvis Ed han lod hånt om, og hvis Pagt han brød, der hos ham i Babel skal han dø.
“‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
17 Og Farao skal ikke hjælpe ham i Krigen med en stor Hær eller en talrig Skare, når der opkastes Stormvold og bygges Belejringstårne til Undergang for mange Mennesker.
Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
18 Thi han lod hånt om Eden og brød Pagten trods givet Håndslag; alt dette gjorde han; han skal ikke undslippe!
Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
19 Sig derfor: Så siger den Herre HERREN: Så sandt jeg lever: Min Ed, som han lod hånt om, og min Pagt, som han brød, vil jeg visselig lade komme over hans Hoved!
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
20 Jeg breder mit Net over ham, så han fanges i mit Garn, og jeg bringer ham til Babel for der at gå i Rette med ham for den Troløshed, han viste mig.
Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
21 Alle hans udvalgte Folk i alle hans Hære skal falde for Sværd, og de, der er til Rest, spredes for alle Vinde; og I skal kende, at jeg, HERREN, har talet.
Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
22 Så siger den Herre HERREN: Så tager jeg selv en Gren af Cederens Top, af dens Skuds Spidser bryder jeg en tynd Kvist og planter den på et højt, knejsende Bjerg.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
23 På Israels høje Bjerg vil jeg plante den, og den skal skyde Grene og bære Løv og blive en herlig Ceder. Under den skal alle vingede Fugle bygge, i dens Grenes Skygge skal de bo.
A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
24 Og alle Markens Træer skal kende, at jeg, HERREN, nedbøjer det høje Træ og ophøjer det lave, udtørrer det friske Træ og lader det tørre blomstre. Jeg, HERREN, har talt og grebet ind.
Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”