< Ezekiel 16 >

1 HERRENs Ord kom til mig således:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Menneskesøn, forehold Jerusalem dets Vederstyggeligheder
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 og sig: Så siger den Herre HERREN til Jerusalem: Dit Udspring og din Oprindelse var i Kanaanæernes Land; din Fader var Amorit, din Moder Hetiterinde.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 Og ved din Fødsel gik det således til: Da du fødtes, blev din Navlestreng ikke skåret over, ej heller blev du tvættet ren med Vand eller gnedet med Salt eller lagt i Svøb.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 Ingen så på dig med så megen Medynk, at han af Medlidenhed gjorde nogen af disse Ting for dig, men du henslængtes på Marken, den Dag du fødtes; således væmmedes man ved din Sjæl.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 Men jeg kom forbi, og da jeg så dig sprælle i Blod, sagde jeg til dig, som du lå der i Blodet: "Du skal leve
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 og vokse som en Urt på Marken!" Og du voksede, blev stor og trådte ind i din Skønheds Fylde; dine Bryster blev faste, og dit Hår voksede; men du var nøgen og bar.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 Så kom jeg forbi og så dig, og se, din Tid var inde, din Elskovstid; og jeg bredte min Kappeflig over dig og tilhyllede din Blusel; så tilsvor jeg dig Troskab og indgik Pagt med dig, lyder det fra den Herre HERREN, og du blev min.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Så tvættede jeg dig med Vand, skyllede Blodet af dig og salvede dig med Olie;
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 jeg klædte dig i broget vævede Klæder, gav dig Sko af Tahasjskind på, bandt Byssusklæde om dit Hoved og hyllede dig i Silke;
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 jeg smykkede dig, lagde Spange om dine Arme og Kæde om din Hals,
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 fæstede en Ring i din Næse, kugler i dine Ører og en herlig krone på dit Hoved;
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 du smykkedes med Guld og - Sølv, din Klædning var Byssus, Silke og broget vævede Klæder; fint Hvedemel, Honning og Olie var din Mad, og du blev såre dejlig og drev det til at blive Dronning.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Dit Ry kom ud blandt Folkene for din Dejligheds Skyld; thi den var fuldendt ved de Smykker, jeg udstyrede dig med, lyder det fra den Herre HERREN.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Men du stolede på din Dejlighed og bolede i Kraft af dit Ry; du udøste din bolerske Attrå over enhver, som kom forbi; du blev hans.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Af dine Klæder tog du og gjorde dig spraglede Offerhøje og bolede på dem.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 Du tog dine Smykker af mit Guld og Sølv, som jeg havde givet dig, og gjorde dig Mandsbilleder og bolede med dem.
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 Du tog dine broget vævede Klæder og hyllede dem deri, og min Olie og Røgelse satte du for dem.
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 Brødet, som jeg havde givet dig - fint Hedemel, Olie og Honning gav jeg dig at spise - satte du for dem til en liflig Duft, lyder det fra den Herre HERREN.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Og du tog dine Sønner og Døtre, som du havde født mig, og slagtede dem til Føde for dem. Var det ikke nok med din Bolen,
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 siden du slagtede mine Sønner og gav dem hen, idet du indviede dem til dem?
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 Og under alle dine Vederstyggeligheder og din Bolen kom du ikke din Ungdoms dage i Hu, da du var nøgen og bar og lå og sprællede i Blod.
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 Og efter al denne din Ondskab - ve dig, ve! lyder det fra den Herre HERREN -
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 byggede du dig en Alterfod og gjorde dig en Offerhøj på alle Torve.
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 Ved hvert Gadehjørne byggede du dig en Offerhøj og vanærede din Dejlighed; du spredte Benene for enhver, som kom forbi, og drev din Bolen vidt.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Du bolede med Ægypterne, dine sværlemmede Naboer, og drev din Bolen vidt og krænkede mig.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Men se, jeg udrakte min Hånd imod dig og unddrog dig, hvad der tilkom dig, og jeg gav dig dine Fjender Filisterindernes Gridskhed i Vold, de, som skammede sig over din utugtige Færd.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Siden bolede du med Assyrerne, umættelig som du var; du bolede med dem, men blev endda ikke mæt.
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Så udstrakte du din Bolen til Kræmmerlandet, Kaldæernes Land, men blev endda ikke mæt.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 Hvor vansmægtede dog dit Hjerte, lyder det fra den Herre HERREN, da du gjorde alt dette, som kun en arg Skøge kan gøre,
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 da du byggede dig en Alterfod ved hvert Gadehjørne og gjorde dig en Offerhøj på hvert Torv. Men du lignede ikke Skøgen i at samle Skøgeløn;
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 hvilken Horkvinde, der tager fremmede i sin Mands Sted! -
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 ellers giver man Skøgen en Gave, men du gav alle dine Elskere Gaver og købte dem til at komme til dig rundt om fra og bole med dig.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 Hos dig var det modsat af, hvad Tilfældet ellers er med Kvinder; ingen løb efter dig for at bole, men du gav Skøgeløn og fik selv ingen; det var det modsatte.
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 Derfor, du Skøge, hør HERRENs Ord!
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 Så siger den Herre HERREN: Fordi din Skam ødtes bort og din Blusel blottedes for dine Elskere ved din Boler, derfor og for alle dine vederstyggelige Afgudsbilleders Skyld og for dine Sønners Blods Skyld, som du gav dem,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 se, derfor vil jeg samle alle dine Elskere, hvem du var til Glæde, både alle dem, du elskede, og alle dem, du hadede; jeg vil samle dem imod dig trindt om fra og blotte din Blusel for dem, så de ser den helt.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 Jeg vil dømme dig efter Horkvinders og Morderskers Ret og lade Vrede og Nidkærhed ramme dig.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 Jeg giver dig i deres Hånd, og de skal nedbryde din Alterfod, ødelægge dine Offerhøje, rive Klæderne af dig, tage dine Smykker og lade dig stå nøgen og bar.
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 De skal sammenkalde en Forsamling imod dig, stene dig og med deres Sværd hugge dig sønder og sammen;
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 de skal sætte Ild på dine Huse og fuldbyrde Dommen over dig i mange Kvinders Påsyn. Jeg gør Ende på din Bolen, og du skal ikke mere komme til at give Skøgeløn.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 Jeg stiller min Vrede på dig, til min Nidkærhed viger fra dig, så jeg får Ro og ikke mere er krænket.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 Fordi du ikke kom dine Ungdoms Dage i Hu, men vakte min Vrede ved alt dette, se, derfor vil jeg gøre Gengæld og lade din Færd komme over dit Hoved, lyder det fra den Herre HERREN. Du skal ikke vedblive at føje Skændsel til alle dine Vederstyggeligheder.
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Se, enhver, som ynder Ordsprog, skal bruge det Ordsprog om dig: "Som Moder så datter!"
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 Du er din Moders Datter, hun lededes ved sin Mand og sine Børn; og du er dine Søstres Søster, de lededes ved deres Mænd og Børn. Eders Moder var Hetiterinde, eders Fader Amorit.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Din store søster var samaria og hendes Døtre norden for dig, og din lille Søster sønden for dig var Sodoma og hendes Døtre.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 På deres Veje vandrede du ikke, og Vederstyggeligheder som deres øvede du ikke; kun en liden Stund, så handlede du endnu værre end de på alle dine Veje.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 Så sandt jeg lever, lyder det fra den Herre HERRE, din Søster Sodoma og hendes Døtre handlede ikke som du og dine Døtre!
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Se, din Søster Sodomas Brøde var Overmod; Brød i Overflod og sorgløs Tryghed blev hende og hendes Døtre til Del, men de rakte ikke den arme og fattige en hjælpende Hånd;
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 de blev hovmodige og øvede Vederstyggelighed for mine Øjne; derfor stødte jeg dem bort, så snart jeg så det.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Heller ikke Samaria syndede halvt så meget som du! Du har øvet flere Vederstyggeligheder end de og retfærdiggjort dine Søstre ved alle de Vederstyggeligheder, du øvede.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Så bær da også du din Skændsel, du, som har skaffet dine Søstre Oprejsning; da dine Synder er vederstyggeligere end deres, står de retfærdigere end du; så skam da også du dig og bær din Skændsel, fordi du har retfærdiggjort dine Søstre.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 Og jeg vil vende deres Skæbne, Sodomas og hendes Døtres og Samarias og hendes Døtres, og jeg vil vende din Skæbne midt iblandt dem,
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 for at du kan bære din Skændsel og blues ved alt, hvad du har gjort, idet du derved skaffede demen Trøst.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 Dine Søstre Sodoma og hendes Døtre og Samaria og hendes Døtre skal blive, hvad de fordum var, og du og dine Døtre, hvad I fordum var.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Din Søster Sodomas Navn tog du ikke i din Mund i dit Overmods Dage,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 da din Blusel endnu ikke var blottet som nu, du Spot for Edoms Kvinder, og alle kvinder deromkring og for Filisternes Kvinder, som hånede dig fra alle Sider!
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Du må bære din Skændsel og dine Vederstyggeligheder, lyder det fra HERREN.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 Ja, så siger den Herre HERREN: Jeg gør med dig, som du har gjort, du, som lod hånt om Eden og brød Pagten.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Men jeg vil ihukomme min Pagt med dig i din Ungdoms Dage og oprette en evig Pagt med dig.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Og du skal komme dine Veje i Hu og blues, når jeg tager dine Søstre, både dem, der er større, og dem, der er mindre end du, og giver dig dem til Døtre, men ikke fordi du var tro i Pagten.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 Jeg opretter min Pagt med dig, og du skal kende, at jeg er HERREN,
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 for at du skal komme det i Hu med Skam og ikke mere kunne åbne din Mund, fordi du blues, når jeg tilgiver dig alt, hvad du har gjort, lyder det fra den Herre HERREN.
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ezekiel 16 >