< Ezekiel 11 >

1 Så løftede Ånden mig og bragte mig til Herrens huses østport, den der vender mod Øst. Og se, ved Indgangen til Porten var der fem og tyve Mænd, og jeg så iblandt dem Jaazanja, Azzurs Søn, og Pelatja, Benajas Søn, Folkets Fyrster.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
2 Og han sagde til mig: "Menneskesøn! Det er de Mænd, som pønser på Uret og lægger onde Råd op i denne By,
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
3 idet de siger: "Er Husene ikke nys bygget? Byen er Gryden, vi Kødet!"
Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
4 Profeter derfor imod dem, profeter, Menneskesøn!
Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
5 Så faldt HERRENs Ånd på mig, og han sagde til mig: Sig: Så siger HERREN: Således taler I, Israels Hus; jeg kender godt, hvad der stiger op i eders Ånd.
Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
6 Mange har I dræbt i denne By; I har fyldt dens Gader med dræbte.
Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
7 Derfor, så siger den Herre HERREN: De, som I dræbte og henslængte i dens Midte, de er Kødet, og Byen er Gryden; men eder vil jeg føre ud af den.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
8 I frygter for Sværd, og Sværd vil jeg bringe over eder, lyder det fra den Herre HERREN.
Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Jeg vil føre eder ud af den og give eder i fremmedes Hånd, og jeg vil holde Dom over eder.
Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
10 For Sværd skal I falde; ved Israels Grænse vil jeg dømme eder. Og I skal kende, at jeg er HERREN.
Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
11 Byen skal ikke være eder en Gryde, og I skal ikke være Kødet deri; ved Israels Grænse vil jeg dømme eder.
Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
12 Og I skal kende, at jeg er HERREN, hvis Vedtægter I ikke fulgte, og hvis Lovbud I ikke levede efter, hvorimod I levede efter eders Nabofolks Lovbud. -
Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
13 Men medens jeg profeterede således, døde Pelatja, Benajas Søn. Da faldt jeg på mit Ansigt og råbte med høj Røst: "Ak, Herre, HERRE, vil du da helt udrydde Israels Rest?"
Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
14 Så kom HERRENs Ord til mig således:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
15 Menneskesøn! Dine Brødre, dine Medfanger og alt Israels Hus, alle de, om hvem Jerusalems Indbyggere siger: "De er langt borte fra HERREN, os er Landet givet i Eje!" -
“Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
16 derfor skal du sige: Så siger den Herre HERREN: Ja, jeg har ført dem langt bort blandt Folkene og spredt dem i Landene, og kun i ringe Måde var jeg dem en Helligdom i de Lande, hvor de kom hen.
“Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
17 Men derfor skal du sige: Så siger den Herre HERREN: Jeg vil samle eder sammen fra Folkeslagene og sanke eder op i Landene, hvor I er spredt, og give eder Israels Jord.
“Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
18 Derhen skal de komme og fjerne alle dets væmmelige Guder og alle dets Vederstyggeligheder;
“Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
19 jeg giver dem et nyt Hjerte og indgiver dem en ny Ånd; jeg tager Stenhjertet ud af deres Legeme og giver dem et Kødhjerte,
Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
20 for at de må følge mine Vedtægter og holde mine Lovbud og gøre efter dem. Så skal de være mit Folk, og jeg vil være deres Gud.
Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
21 Men hines Hjerter holder sig til deres væmmelige Guder og deres Vederstyggeligheder; dem gengælder jeg deres Færd, lyder det fra den Herre HERREN.
Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
22 Så løftede keruberne Vingerne og samtidig Hjulene; og Israels Guds Herlighed var oven over dem.
Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
23 Og HERRENs Herlighed steg op fra Byen og stillede sig på Bjerget østen for.
Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
24 Derpå løftede Ånden mig og bragte mig ved Guds Ånd i Synet til de landflygtige i Kaldæa; og Synet, som jeg havde skuet, steg op og svandt bort.
Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
25 Så kundgjorde jeg de landflyggige alle de Ord, HERREN havde åbenbaret mig.
na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.

< Ezekiel 11 >