< 2 Mosebog 33 >

1 HERREN sagde til Moses: "Drag nu bort herfra med Folket, som du førte ud af Ægypten, til det Land, jeg tilsvor Abraham, Isak og Jakob med de Ord: Dit Afkom vil jeg give det!
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
2 Jeg sender en Engel foran dig, og han skal drive Kana'anæerne, Amoriterne, Hetiterne, Perizziterne, Hivviterne og Jebusiterne bort
Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
3 til et Land, der flyder med Mælk og Honning. Men selv vil jeg ikke drage med i din Midte, thi du er et halsstarrigt Folk; drog jeg med, kunde jeg tilintetgøre dig undervejs!"
Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
4 Da Folket hørte denne onde Tidende, sørgede de, og ingen tog sine Smykker på.
Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
5 Da sagde HERREN til Moses: "Sig til Israeliterne; I er et halsstarrigt Folk! Vandrede jeg kun et eneste Øjeblik i din Midte, måtte jeg tilintetgøre dig. Tag du dine Smykker af, så skal jeg tænke over, hvad jeg vil gøre for dig!"
Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
6 Da aflagde Israeliterne deres Smykker fra Horebs Bjerg af.
Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
7 Moses plejede at tage Teltet og slå det op udenfor Lejren i nogen Afstand derfra; han gav det Navnet "Åbenbaringsteltet". Enhver som vilde rådspørge HERREN, gik ud til Åbenbaringsteltet uden for Lejren.
Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
8 Men hver Gang Moses gik ud til teltet, rejste alt Folket sig op og stillede sig alle ved Indgangen til deres Telte og så efter Moses, indtil han kom ind i Teltet.
A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
9 Og når Moses kom ind Teltet, sænkede Skystøtten sig og stillede sig ved Indgangen til Teltet; da talede HERREN med Moses.
Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
10 Men når alt Folket så Skystøtten stå ved Indgangen til Teltet, rejste de sig alle op og tilbad ved Indgangen til deres Telte.
Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
11 Så talede HERREN med Moses Ansigt til Ansigt, som når den ene Mand taler med den anden, og derpå vendte Moses tilbage til Lejren; men hans Medhjælper Josua, Nuns Søn, en ung Mand, veg ikke fra Teltet.
Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
12 Moses sagde til HERREN: "Se, du siger til mig: Før dette Folk frem! Men du har ikke ladet mig vide, hvem du vil sende med mig; og dog har du sagt: Jeg kender dig ved Navn, og du har fundet Nåde for mine Øjne!
Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
13 Hvis jeg nu virkelig har fundet Nåde for dine Øjne, så lær mig dine Veje at kende, at jeg kan kende dig og finde Nåde for dine Øjne; tænk dog på, at dette Folk er dit Folk!"
In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
14 Han svarede: "Skal mit Åsyn da vandre med, og skal jeg således føre dig til Målet?"
Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
15 Da sagde Moses til ham: "Hvis dit Åsyn ikke vandrer med, så lad os ikke drage herfra!
Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
16 Hvorpå skal det dog kendes. at jeg har fundet Nåde for dine Øjne, jeg og dit Folk? Mon ikke på, at du vandrer med os, og der således vises os, mig og dit Folk, en Udmærkelse fremfor alle andle Folkeslag på Jorden?"
Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
17 HERREN svarede Moses: "Også hvad du der siger, vil jeg gøre, thi du har fundet Nåde for mine Øjne, og jeg kalder dig ved Navn."
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
18 Da sagde Moses: "Lad mig dog skue din Herlighed!"
Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
19 Han svarede: "Jeg vil lade al min Rigdom drage forbi dig og udråbe HERRENs Navn foran dig, thi jeg viser Nåde, mod hvem jeg vil, og Barmhjertighed, mod hvem jeg vil!"
Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
20 Og han sagde: "Du kan ikke skue mit Åsyn, thi intet Menneske kan se mig og leve."
Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
21 Og HERREN sagde: "Se, her er et Sted i min Nærhed, stil dig på Klippen der!
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
22 Når da min Herlighed drager forbi, vil jeg lade dig stå i Klippehulen, og jeg vil dække dig 1ned min Hånd, indtil jeg er kommet forbi.
A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
23 Så tager jeg min Hånd bort, og da kan du se mig bagfra; men mit Åsyn kan ingen skue!"
Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”

< 2 Mosebog 33 >