< 2 Mosebog 3 >

1 Moses vogtede nu Småkvæget for sin Svigerfader Jetro, Præsten i Midjan, og drev engang Småkvæget hen hinsides Ørkenen og kom til Guds Bjerg Horeb.
Ana nan wata rana Musa yana kiwon tumakin Yetro surukinsa, firist na Midiyan, sai ya bi da tumaki zuwa gefe mai nisa a cikin hamada, har ya zo Horeb, dutsen Allah.
2 Da åbenbarede HERRENs Engel sig for ham i en Ildslue, der slog ud af en Tornebusk, og da han så nærmere til, se, da stod Tornebusken i lys Lue, uden at den blev fortæret.
A can mala’ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a ƙaramin itace. Musa ya lura cewa ko da yake wuta na ci ƙaramin itacen, amma bai ƙone ba.
3 Da sagde Moses: "Lad mig gå hen og se på dette underfulde Skue, hvorfor Tornebusken ikke brænder op."
Sai Musa ya ce, “Wannan abin mamaki ne, don me wannan itace bai ƙone ba? Bari in matso kusa in gani.”
4 Men da HERREN så, at han gik hen for at se derpå, råbte Gud til ham fra Tornebusken: "Moses, Moses!" Og han svarede: "Se, her er jeg!"
Da Ubangiji ya ga Musa ya matso don yă duba, sai Allah ya yi kira daga cikin ƙaramin itacen ya ce, “Musa! Musa!” Sai Musa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
5 Da sagde han: "Kom ikke nærmere! Drag dine Sko af dine Fødder, thi det Sted, du står på, er hellig Jord!"
Allah ya ce, “Kada ka zo kusa, tuɓe takalmanka, gama inda kake tsaye, wuri ne mai tsarki.”
6 Og han sagde: "Jeg er din Faders Gud, Abrahams Gud, Isaks Gud og Jakobs Gud." Da skjulte Moses sit Ansigt, thi han frygtede for at skue Gud.
Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub.” Da jin wannan, sai Musa ya ɓoye fuskarsa, domin ya ji tsoro yă dubi Allah.
7 Derpå sagde HERREN: "Jeg har set mit Folks Elendighed i Ægypten, og jeg har hørt deres Klageskrig over deres Undertrykkere, ja, jeg kender deres Lidelser;
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.
8 og jeg er steget ned for at udfri dem af Ægyptens Hånd og føre dem bort fra dette Land til et godt og vidtstrakt Land, til et Land, der flyder med Mælk og Honning, til Kana'anæernes, Hetiternes, Amoriternes, Perizzitemes, Hivviternes og Jebusiternes Egn.
Saboda haka na sauko domin in cece su daga hannun Masarawa, in kuma fitar da su daga ƙasar Masar, in kai su ƙasa mai kyau mai fāɗi, ƙasa mai zub da madara da zuma, inda Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa suke.
9 Se, nu er Israeliternes Klageskrig nået til mig, og jeg har også set den Trængsel, Ægypterne har bragt over dem.
Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su
10 Derfor vil jeg nu sende dig til Farao, og du skal føre mit Folk, Israeliterne, ud af Ægypten!"
To, fa, sai ka tafi. Ina aikan ka wurin Fir’auna don ka fitar da mutanena Isra’ilawa daga Masar.”
11 Men Moses sagde til Gud: "Hvem er jeg, at jeg skulde kunne gå til Farao og føre Israeliterne ud af Ægypten?"
Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi wurin Fir’auna, in kuma fitar da Isra’ilawa daga Masar?”
12 Han svarede: "Jo, jeg vil være med dig! Og dette skal være dig Tegnet på, at det er mig, der har sendt dig: Når du har ført Folket ud af Ægypten, skal I dyrke Gud på dette Bjerg!"
Sai Allah ya ce, “Zan kasance da tare kai. Wannan kuwa za tă zama alama a gare ka cewa Ni na aike ka. Bayan ka fitar da mutanen daga Masar, za ku yi sujada ga Allah a kan dutsen nan.”
13 Men Moses sagde til Gud: "Når jeg kommer til Israeliterne og siger dem, at deres Fædres Gud har sendt mig til dem, hvad skal jeg så svare dem, hvis de spørger om hans Navn7"
Musa ya ce wa Allah, “A ce ma na tafi wurin Isra’ilawa na ce musu, ‘Allah na kakanninku ya aiko ni wurinku,’ in suka tambaye ni, ‘Mene ne sunansa?’ Me zan ce?”
14 Gud svarede Moses: "Jeg er den, jeg er!" Og han sagde: "Således skal du sige til Israeliterne: JEG ER har sendt mig til eder!"
Allah ya ce wa Musa, “NI NE wanda NINE. Abin da za ka faɗa wa Isra’ilawa ke nan cewa, ‘NI NE, ya aiko ni wurinku.’”
15 Og Gud sagde fremdeles til Moses: "Således skal du sige til Israeliterne: HERREN, eders Fædres Gud, Abrahams Gud, Isaks Gud og Jakobs Gud, har sendt mig til eder; dette er mit Navn til evig Tid, og således skal jeg kaldes fra Slægt til Slægt.
Allah ya kuma ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ubangiji, Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub, ya aiko ni wurinku.’ Wannan shi ne sunana har abada, sunan da za a tuna da ni daga tsara zuwa tsara ke nan.
16 Gå nu hen og kald Israels Ældste sammen og sig til dem: HERREN, eders Fædres Gud, Abrahams, Isaks og Jakobs Gud, har åbenbaret sig for mig og sagt: Jeg har givet Agt på eder og på, hvad man har gjort imod eder i Ægypten,
“Tafi ka tattara dattawan Isra’ila, ka ce musu, ‘Ubangiji, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, ya bayyana a gare ni ya ce, Na lura da ku, na kuma ga abubuwan da ake yi muku a Masar.
17 og jeg har sat mig for at føre eder ud af Ægyptens Elendighed til Kana'anæernes, Hetiternes, Amoriternes, Perizziternes, Hivviternes og Jebusiternes Land, til et Land, der flyder med Mælk og Honning!
Na kuma yi alkawari, zan fitar da ku daga azabarku a Masar zuwa ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasa mai zub da madara da zuma.’
18 De vil høre på dig, og du skal sammen med Israels Ældste gå til Ægypterkongen, og I skal sige til ham: HERREN, Hebræernes Gud, har mødt os, tillad os derfor at drage tre Dagsrejser ud i Ørkenen og ofre til HERREN vor Gud!
“Dattawan Isra’ila za su saurare ka. Sa’an nan da kai da dattawan Isra’ila, za ku tafi wurin sarkin Masar, ku ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya sadu da mu. Bari mu yi tafiyar kwana uku zuwa cikin hamada domin mu yi hadaya wa Ubangiji Allahnmu.’
19 Jeg ved vel, at Ægypterkongen ikke vil tillade eder at drage bort uden med Magt;
Amma na san cewa sarkin Masar ba zai yarda ku tafi ba, sai hannu mai ƙarfi ya tilasta shi.
20 men jeg skal udrække min Hånd og ramme Ægypten med alle mine Undergerninger, som jeg vil gøre der; så skal han give eder Lov til at drage af Sted.
Saboda haka zan miƙa hannuna in bugi Masarawa da duk al’ajaban da zan aikata a cikinsu. Bayan haka zai bar ku, ku tafi.
21 Og jeg vil stemme Ægypterne gunstigt mod dette Folk, så at I, når I drager bort, ikke skal drage bort med tomme Hænder.
“Zan kuma sa mutanen su sami tagomashi daga wurin Masarawa, saboda sa’ad da za ku fita, ba za ku fita hannu wofi ba.
22 Enhver Kvinde skal bede sin Naboerske og de Kvinder, som er til Huse hos hende, om Sølv og Guldsmykker og Klæder, og I skal give eders Sønner og Døtre det på. Således skal I tage Bytte fra Ægypterne."
Kowace mace ta tambayi maƙwabciyarta, da kuma duk wata macen da take cikin gidanta, kayayyakin azurfa da na zinariya da kuma na riguna, waɗanda za ku sa wa’ya’yanku maza da mata. Ta haka nan za ku washe Masarawa.”

< 2 Mosebog 3 >