< 2 Mosebog 18 >

1 Da Jetro, Præsten i Midjan, Moses's Svigerfader, hørte om alt, hvad Gud havde gjort for Moses og hans Folk Israel, hvorledes HERREN havde ført Israel ud af Ægypten,
Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
2 tog Jetro, Moses's Svigerfader, Zippora, Moses's Hustru, som han havde sendt hjem,
Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
3 tillige med hendes to Sønner. Af dem hed den ene Gersom; "thi", havde han sagt, "jeg er blevet Gæst i et fremmed Land";
da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
4 og den anden hed Eliezer; "thi", havde han sagt, "min Faders Gud har været min Hjælp og frelst mig fra Faraos Sværd!"
ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
5 Og Jetro, Moses's Svigerfader, kom med hans Sønner og Hustru til Moses i Ørkenen, hvor han havde slået Lejr ved Guds Bjerg,
Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
6 og han lod Moses melde: "Jetro, din Svigerfader, kommer til dig med din Hustru og hendes to Sønner!"
Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
7 Da gik Moses sin Svigerfader i Møde, bøjede sig for ham og kyssede ham; og da de havde hilst på hinanden, gik de ind i Teltet.
Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
8 Moses fortalte sin Svigerfader om alt, hvad HERREN havde gjort ved Farao og Ægypten for Israels Skyld, og om alle de Besværligheder, der havde mødt dem undervejs, og hvorledes HERREN havde frelst dem.
Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
9 Da glædede Jetro sig over alt det gode, HERREN havde gjort mod Israel, idet han havde frelst dem af Ægypternes Hånd.
Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
10 Og Jetro sagde: "Lovet være HERREN, som har frelst eder af Ægypternes og Faraos. Hånd!"
“Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
11 Nu ved jeg, at HERREN er større end alle Guder, thi netop ved det, de i deres Overmod foretog sig imod dem, frelste han Folket af Ægypternes Hånd.
Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
12 Derpå udtog Jetro, Moses's Svigerfader, Brændofre og Slagtofre til Gud; og Aron og alle Israels Ældste kom for at holde Måltid for Guds Åsyn med Moses's Svigerfader.
Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
13 Næste Morgen tog Moses Sæde for at holde Ret for Folket, og Folket stod omkring Moses fra Morgen til Aften.
Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
14 Men da Moses's Svigerfader så alt det Arbejde, han havde med Folket, sagde han: "Hvad er dog det for et Arbejde, du har med Folket? Hvorfor sidder du alene til Doms, medens alt Folket står omkring dig fra Morgen til Aften?"
Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
15 Moses svarede sin Svigerfader: "Jo, Folket kommer til mig for at rådspørge Gud;
Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
16 når de har en Retssag, kommer de til mig, og jeg dømmer Parterne imellem og kundgør dem Guds Anordninger og Love."
Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
17 Da sagde Moses's Svigerfader til ham: "Det er ikke klogt, som du bærer dig ad med det.
Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
18 På den Måde bliver jo både du selv og Folket der omkring dig ganske udmattet, thi det Arbejde er dig for anstrengende, du kan ikke overkomme det alene.
Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
19 Læg dig nu på Sinde, hvad jeg siger; jeg vil give dig et Råd, og Gud skal være med dig: Du skal. selv træde frem for Gud på Folkets Vegne og forelægge Gud de forefaldende Sager;
Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
20 og du skal indskærpe dem Anordningerne og Lovene og lære dem den Vej, de skal vandre, og hvad de har at gøre.
Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
21 Men du skal af hele Folket udvælge dig dygtige Mænd, som frygter Gud, Mænd, som er til at lide på og hader uretfærdig Vinding, og dem skal du sætte over dem som Forstandere, nogle over tusinde, andre over hundrede, andre over halvtredsindstyve, andre over ti;
Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
22 lad dem til Stadighed holde Ret for Folket. Alle vigtigere Sager skal de forebringe dig, men alle mindre Sager skal de selv afgøre. Let dig således Arbejdet og lad dem komme til at bære Byrden med dig.
Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
23 Dersom du handler således og Gud vil det så, kan du holde ud, og alt Folket der kan gå tilfreds hjem."
In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
24 Moses fulgte sin Svigerfaders Råd og gjorde alt, hvad han foreslog.
Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
25 Og Mose's udvalgte dygtige Mænd af hele Israel og gjorde dem til Øverster over Folket, til Forstandere, nogle over tusinde, andre over hundrede, andre over halvtredsindstyve, andre over ti.
Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
26 De holdt derpå til Stadighed Ret for Folket; de vanskelige Sager forebragte de Moses, men alle mindre Sager afgjorde de selv.
Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
27 Derpå tog Moses Afsked med sin Svigerfader, og denne begav sig til sit Land.
Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.

< 2 Mosebog 18 >