< 2 Mosebog 10 >

1 Derpå sagde HERREN til Moses: "Gå til Farao! Thi jeg har forhærdet hans og hans Tjeneres Hjerte, at jeg kan komme til at gøre disse mine Tegn iblandt dem,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 for at du må kunne fortælle din Søn og din Sønnesøn, hvorledes jeg handlede med Ægypterne, og om de Tegn, jeg gjorde iblandt dem; så skal I kende, at jeg er HERREN."
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Da gik Moses og Aron til Farao og sagde til ham: "Så siger HERREN, Hebræernes Gud: Hvor længe vil du vægre dig ved at ydmyge dig for mig? Lad mit Folk rejse, at de kan dyrke mig!
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 Men hvis du vægrer dig ved at lade mit Folk rejse, se, da vil jeg i Morgen sende Græshopper over dine Landemærker,
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 og de skal skjule Landets Overflade, så man ikke kan se Jorden, og opæde Resten af det, som er blevet tilovers for eder efter Haglen, og opæde alle eders Træer, som gror på Marken;
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 og de skal fylde dine Huse og alle dine Tjeneres og alle Ægypternes Huse således, at hverken dine Fædre eller dine Fædres Fædre nogen Sinde har oplevet Mage dertil, fra den Dag de kom til Verden og indtil denne Dag!" Dermed vendte han sig bort og forlod Farao.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Men Faraos Tjenere sagde til ham: "Hvor længe skal denne Mand styrte os i Ulykke? Lad dog disse Mennesker rejse og lad dem dyrke HERREN deres Gud! Har du endnu ikke indset, at Ægypten går til Grunde?"
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 Moses og Aron blev nu hentet tilbage til Farao, og han sagde til dem: "Drag af Sted og dyrk HERREN eders Gud! Men hvem er det nu, der vil af Sted?"
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Moses svarede: "Med vore Børn og vore gamle vil vi drage af Sted, med vore Sønner og vore Døtre, vort Småkvæg og vort Hornkvæg vil vi drage af Sted, thi vi skal fejre HERRENs Højtid."
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 Da sagde han til dem: "HERREN være med eder, om jeg lader eder rejse sammen med eders Kvinder og Børn! Der ser man, at I har ondt i Sinde!
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 Nej men I Mænd kan drage bort og dyrke HERREN; det var jo det, I ønskede!" Derpå jog man dem bort fra Farao.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 Da sagde HERREN til Moses: "Ræk din Hånd ud over Ægypten og få Græshopperne til at komme; de skal komme over Ægypten og opæde alt, hvad der vokser i Landet, alt, hvad Haglen har levnet!"
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Moses rakte da sin Stav ud over Ægypten, og HERREN lod en Østenstorm blæse over Landet hele den Dag og den påfølgende Nat; og da det blev Morgen, førte Østenstormen Græshopperne med sig.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 Da kom Græshopperne over hele Ægypten, og de slog sig ned i hele Ægyptens Område i uhyre Mængder; aldrig før havde der været så mange Græshopper, og ingen Sinde mere skal der komme så mange.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 Og de skjulte hele Jordens Overflade, så Jorden blev sort af dem, og de opåd alt, hvad der voksede i Landet, og alle Træfrugter, alt, hvad Haglen havde levnet, og der blev intet grønt tilbage på Træerne eller på Markens Urter i hele Ægypten.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Da lod Farao skyndsomt Moses og Aron kalde til sig og sagde: "Jeg har syndet mod HERREN eders Gud og mod eder!
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 Men tilgiv mig nu min Synd denne ene Gang og gå i Forbøn hos eders Gud, at han dog blot vil tage denne dødbringende Plage fra mig!"
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Da gik Moses bort fra Farao og bad til HERREN.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 Og HERREN lod Vinden slå om til en voldsom Vestenvind, som tog Græshopperne og drev dem ud i det røde Hav, så der ikke blev en eneste Græshoppe tilbage i hele Ægyptens Område.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 Men HERREN forhærdede Faraos Hjerte, så han ikke lod Israeliterne rejse.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Derpå sagde HERREN til Moses: "Ræk din Hånd op mod Himmelen, så skal der komme et Mørke over Ægypten, som man kan tage og føle på!"
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Da rakte Moses sin Hånd op mod Himmelen, og der kom et tykt Mørke i hele Ægypten i tre Dage;
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 den ene kunde ikke se den anden, og ingen flyttede sig af Stedet i tre Dage; men overalt, hvor Israeliterne boede, var det lyst.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 Da lod Farao Moses kalde og sagde: "Drag hen og dyrk HERREN. Dog skal eders Småkvæg og Hornkvæg blive tilbage, men eders Kvinder og Børn må I tage med."
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Men Moses sagde: "Du må også overlade os Slagtofre og Brændofre, som vi kan bringe HERREN vor Gud;
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 også vore Hjorde må vi have med, ikke en Klov må blive tilbage, thi dem har vi Brug for, når vi skal dyrke HERREN vor Gud, og vi ved jo ikke, hvor meget vi behøver dertil, før vi kommer til Stedet."
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 Da forhærdede HERREN Faraos Hjerte, så han nægtede at lade dem rejse.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 Og Farao sagde til ham: "Gå bort fra mig og vogt dig for at komme mig for Øje mere; thi den Dag du kommer mig for Øje, er du dødsens!"
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Da sagde Moses: "Du har sagt det, jeg skal ikke mere komme dig for Øje!"
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< 2 Mosebog 10 >