< 5 Mosebog 5 >

1 Moses kaldte hele Israel sammen og sagde til dem: Hør, Israel, de Anordninger og Lovbud, som jeg kundgør eder i Dag! Lær dem og hold dem omhyggeligt.
Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
2 HERREN vor Gud sluttede en Pagt med os ved Horeb.
Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
3 Det var ikke med vore Fædre, HERREN sluttede den Pagt, men med os, vi, der i Dag er her til Stede, alle vi, der er i Live.
Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
4 Ansigt til Ansigt talede HERREN med eder på Bjerget ud fra Ilden.
Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
5 Jeg stod dengang som Mellemmand mellem HERREN og eder og kundgjorde eder HERRENs Ord; thi I var bange for Ilden og turde ikke stige op på Bjerget.
(A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
6 Han sagde: Jeg er HERREN din Gud, som førte dig ud af Ægypten, af Trællehuset.
“Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
7 Du må ikke have andre Guder end mig.
“Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
8 Du må ikke gøre dig noget udskåret Billede eller noget Afbillede af det, som er oppe i Himmelen eller nede på Jorden eller i Vandet under Jorden;
Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
9 du må ikke tilbede eller dyrke det, thi jeg HERREN din Gud er en nidkær Gud, der indtil tredje og fjerde Led straffer Fædres Brøde på Børn af dem, som hader mig,
Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
10 men i tusind Led viser Miskundhed mod dem, der elsker mig og holder mine Bud!
Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
11 Du må ikke misbruge HERREN din Guds Navn, thi HERREN lader ikke den ustraffet, der misbruger hans Navn!
Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
12 Tag Vare på Hviledagen, så du holder den hellig, således som HERREN din Gud har pålagt dig!
Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
13 I seks Dage skal du arbejde og gøre al din Gerning,
Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
14 men den syvende Dag skal være Hviledag for HERREN din Gud; da må du intet Arbejde udføre, hverken du selv, din Søn eller Datter, din Træl eller Trælkvinde, din Okse eller dit Æsel eller noget af dit Kvæg eller den fremmede inden dine Porte, for at din Træl og Trælkvinde kan hvile ud ligesom du selv.
amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
15 Kom i Hu, at du selv var Træl i Ægypten, og at HERREN din Gud førte dig ud derfra med stærk Hånd og udstrakt Arm; det er derfor, HERREN din Gud har pålagt dig at fejre Hviledagen!
Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
16 Ær din Fader og din Moder, således som HERREN din Gud har pålagt dig, for at du kan få et langt Liv, og det må gå dig vel i det Land, HERREN din Gud vil give dig.
Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
17 Du må ikke slå ihjel!
Kada ka yi kisankai.
18 Du må ikke bedrive Hor!
Kada ka yi zina.
19 Du må ikke stjæle!
Kada ka yi sata.
20 Du må ikke sige falsk Vidnesbyrd imod din Næste!
Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
21 Du må ikke begære din Næstes Hustru. Du må ikke attrå din Næstes Hus, hans Mark, hans Træl eller Trælkvinde, hans Okse eller Æsel eller noget, der hører din Næste til!
Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
22 Disse Ord talede HERREN til hele eders Forsamling på Bjerget ud fra Ilden, Skyen og Mulmet med vældig Røst uden at føje noget til; og han skrev dem op på to Stentavler og gav mig dem.
Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
23 Men da I hørte Røsten, der lød ud fra Mørket, medens Bjerget stod i lys Lue, kom I, alle Overhovederne for eders Stammer og eders Ældste, hen til mig
Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
24 og sagde: "Se, HERREN vor Gud har ladet os skue sin Herlighed og Storhed, og hans Røst har vi hørt ud fra Ilden; i Dag har vi oplevet, at Gud kan tale med Mennesker, uden at de dør.
Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
25 Men hvorfor skal vi dø? Thi denne vældige Ild vil fortære os; hvis vi skal blive ved at høre på HERREN vor Guds Røst, må vi dø!
Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
26 Thi hvilken dødelig har nogen Sinde som vi hørt den levende Guds Røst ud fra Ilden og levet?
Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
27 Træd du hen og hør alt, hvad HERREN vor Gud siger; siden skal du så sige os alt, hvad HERREN vor Gud taler til dig, og vi skal høre det og gøre derefter."
Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
28 Og da HERREN hørte, hvorledes I talte til mig, sagde han til mig: "Jeg har hørt, hvad dette Folk siger til dig, og alt, hvad de har sagt til dig, er ret;
Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
29 gid de alle Dage må have et sådant Hjerte, at de frygter mig og holder alle mine Bud, for at det må gå dem og deres Børn vel evindelig.
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
30 Gå derfor hen og byd dem at vende tilbage til deres Telte;
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
31 men bliv du stående her hos mig, så skal jeg kundgøre dig alle Budene, Anordningerne og Lovbudene, som du skal lære dem, og som de skal holde i det Land, jeg vil give dem i Eje!"
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
32 Gør derfor omhyggeligt således, som HERREN eders Gud har pålagt eder, uden at vige til højre eller venstre;
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
33 følg altid den Vej, som HERREN eders Gud har pålagt eder at gå, at I kan blive i Live og få det godt og leve længe i det Land, I skal tage i Besiddelse!
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.

< 5 Mosebog 5 >