< 5 Mosebog 32 >

1 Lyt til, I Himle, lad mig tale, Jorden høre mine Ord!
Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
2 Lad dryppe som Regn min Lære, lad flyde som Dug mit Ord, som Regnskyl på unge Spirer, som Regnens Dråber på Græs.
Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
3 Thi HERRENs Navn vil jeg forkynde, Ære skal I give vor Gud!
Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
4 Han er Klippen, fuldkomment hans Værk, thi alle hans Veje er Retfærd! En trofast Gud, uden Svig, retfærdig og sanddru er Han.
Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
5 Skændselsmennesker sveg ham, en forvent og vanartet Slægt.
Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
6 Er det sådan, I lønner HERREN? Du tåbelige, uvise Folk! Er han ej din Fader og Skaber, den, som gjorde og danned dig?
Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
7 Kom Fortidens Dage i Hu, agt på henfarne Slægters År; spørg din Fader, han skal berette, dine gamle, de skal fortælle dig!
Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
8 Da den Højeste gav Folkene Eje, satte Skel mellem Menneskenes Børn, bestemte han Folkenes Grænser efter Tallet på Guds Sønner,
Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
9 men HERRENs Del blev Jakob, Israel hans tilmålte Lod.
Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
10 Han fandt det i Ørkenlandet, i Ødemarken, blandt Ørkenens Hyl; han værnede det med vågent Øje og vogtede det som sin Øjesten.
A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
11 Som Ørnen, der purrer sin Yngel ud og svæver over sine Unger, løftede han det på sit Vingefang og bar det på sine Vinger.
kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
12 HERREN var dets eneste Fører, ingen fremmed Gud var hos ham.
Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
13 Han lod det færdes over Landets Høje, nærede det med Markens Frugter, lod det suge Honning af Klippen og Olie af Bjergets Flint,
Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
14 Surmælk fra Køer, Mælk fra Småkvæg, dertil Fedt af Lam og Vædre, af Tyre fra Basan og Bukke og Hvedens Fedme tillige, og Drueblod drak du, Vin.
da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
15 Men da Jesjurun blev fed, slog han bagud, du blev fed, du blev tyk, du blev mæsket; da forskød han Gud, sin Skaber, lod hånt om sin Frelses Klippe.
Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
16 De æggede ham med fremmede, med Vederstyggeligheder tirrede de ham;
Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
17 de ofred til Dæmoner, der ej er Guder, til Guder, de ej før kendte til; til nye, der nys var kommet frem, og som ej eders Fædre frygtede.
Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
18 Klippen, der avled dig, slog du af Tanke og glemte den Gud, der fødte dig!
Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
19 Da HERREN så det, forstødte han dem af Græmmelse over sine Børn
Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
20 og sagde: "Jeg vil skjule mit Åsyn for dem og se, hvad Ende det tager med dem; thi de er en bundfalsk Slægt, Børn, som er uden Troskab;
Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
21 de ægged mig med det der ikke er Gud, tirrede mig ved deres tomme Gøgl: Jeg vil ægge dem med det, der ikke er et Folk, tirre dem ved et Folk af Dårer.
Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
22 Thi der flammer en Ild i min Vrede, som brænder til Dødsrigets Dyb; den fortærer Jorden med dens Grøde og antænder Bjergenes Grunde. (Sheol h7585)
Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
23 Jeg hober Ulykker over dem og opbruger mine Pile imod dem.
“Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
24 De udmagres af Sult og hentæres af Pestglød og giftig Sot; så sender jeg Vilddyrs Tænder og Slangers Gift imod dem.
Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
25 Ude slår Sværdet Børnene ned og inde i Kamrene Rædselen både Yngling og Jomfru, diende Børn og grånende Mænd.
Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
26 Jeg satte mig for at blæse dem bort og slette deres Minde blandt Mennesker ud,
Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
27 men jeg frygtede, at Fjenden skulde volde mig Græmmelse, deres Avindsmænd tage fejl og tænke: Det var vor egen Hånd, der var stærk, ej HERREN, der gjorde alt dette.
Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
28 Thi de er et rådvildt Folk, og i dem er der ikke Forstand.
Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
29 Var de vise, forstod de det og indså, hvad der venter dem selv!
A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
30 Hvor skulde een kunne forfølge tusind, og to slå ti Tusind på Flugt, hvis ikke deres klippe havde solgt dem og HERREN givet dem til Pris!
Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
31 Thi deres Klippe er ikke som vor, det ved vore Fjender bedst selv!
Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
32 Thi fra Sodoma stammer deres Vinstok og fra Gomorras Marker; deres Druer er giftige Druer, og beske er deres Klaser;
Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
33 som Dragegift er deres Vin, som Øglers gruelige Edder.
Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
34 Er ej dette forvaret hos mig, forseglet i mine Gemmer
“Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
35 til Hævnens og Regnskabets Dag, den Stund, deres Fod skal vakle? Thi deres Undergangs Dag stunder til; hvad der venter dem, kommer i Hast."
Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
36 Thi Ret skaffer HERREN sit Folk og forbarmer sig over sine Tjenere, thi han ser, deres kraft er brudt, det er ude med hver og en.
Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
37 Da spørger han: "Hvor er nu deres Gud, Klippen, på hvem de forlod, sig,
Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
38 som åd deres, Slagtofres Fedme og drak deres Drikofres Vin? Lad dem rejse sig og hjælpe eder, lad dem være eder et Skjul!
allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
39 Erkend nu, at jeg, jeg er Gud uden anden Gud ved min Side. Jeg døder, jeg gør levende, jeg sårer, og jeg læger, "g ingen kan frelse fra min Hånd.
“Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
40 Thi jeg løfter min Hånd mod Himlen og siger: Så sandt jeg lever evindelig,
Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
41 jeg hvæsser mit lynende Sværd, og min Hånd tager fat på Dommen, jeg hævner mig på mine Fjender, øver Gengæld mod mine Avindsmænd.
sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
42 Mine Pile gør jeg drukne af Blod, og mit Sværd skal svælge i Kød, i faldnes og fangnes Blod og fjendtlige Høvdingers Hoveder!"
Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
43 I Folkeslag, pris hans Folk, thi han hævner sine Tjeneres Blod; han hævner sig på sine Fjender, og skaffer sit Folks Land Soning!
Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
44 Og Moses kom og fremsagde hele denne Sang for Folket, han og Josua, Nuns Søn.
Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
45 Og da Moses var færdig med at fremsige alle disse Ord for hele Israel,
Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
46 sagde han til dem: "Læg eder alle de Ord på Sinde, som jeg i Dag har vidnet imod eder, for at du kan pålægge dine Sønner dem, at de omhyggeligt må handle efter alle denne Lovs Bud;
ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
47 thi det er ikke tomme Ord uden Betydning for eder, men af dem afhænger eders Liv, og ved at følge det Ord skal I få et langt Liv i det Land, som l skal ind og tage i Besiddelse efter at være gået over Jordan."
Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
48 Selv samme Dag talede HERREN til Moses og sagde:
A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
49 "Stig op på Abarimbjerget der, Nebobjerget i Moabs Land over for Jeriko, og se ud over Kana'ans Land, som jeg vil give Israelitterne i Eje!
“Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
50 Og så skal du dø på det Bjerg, du bestiger, og samles til din Slægt, ligesom din Broder Aron døde på Bjerget Hor og samledes til sin Slægt,
A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
51 fordi I handlede troløst imod mig iblandt Israelitterne ved Merihat Kadesjs Vand i Zins Ørken, fordi I ikke helligede mig iblandt Israelitterne.
Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
52 Thi her ovre fra skal du se ud over Landet, men du skal ikke komme derind, ind i det Land, jeg vil give Israelitterne!
Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”

< 5 Mosebog 32 >