< 5 Mosebog 3 >
1 Derpå brød vi op og drog mod Basan. Og Kong Og af Basan rykkede med alle sine Krigere ud imod os til Kamp ved Edrei.
Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
2 Da sagde HERREN til mig: "Frygt ikke for ham, thi jeg giver ham i din Hånd tillige med hele hans Folk og Land, og du skal gøre ved ham, som du gjorde ved Sihon, Amoriterkongen i Hesjbon."
Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
3 Så gav HERREN vor Gud også kong Og af Basan og alle hans Krigere i vor Hånd, og vi slog ham, så ikke en eneste undslap.
Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
4 Vi indtog dengang alle hans Byer; der var ikke een By, vi ikke fratog dem, i alt tresindstyve Byer, hele Landskabet Argob, Ogs Kongerige i Basan,
A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
5 lutter Byer, der var befæstet med høje Mure, Porte og Portslåer, foruden de mange åbne Byer;
Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
6 og vi lagde Band på dem, ligesom vi havde gjort ved Kong Sihon i Hesjbon, i enhver By lagde vi Band på Mænd, Kvinder og Børn;
Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
7 men alt Kvæget, og hvad vi røvede fra Byerne, tog vi selv som Bytte.
Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
8 Således erobrede vi dengang Landet fra de to Amoriterkonger hinsides Jordan fra Arnonfloden til Hermonbjerget
A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
9 Zidonierne kalder Hermon Sirjon, men Amoriterne kalder det Senir
(Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
10 alle Byerne på Højsletten, hele Gilead og hele Basan lige til Salka og Edrei, Byer i kong Ogs Rige i Basan.
Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
11 Thi Kong Og af Basan var den eneste, der endnu var tilbage af Refaiterne; hans Kiste, en Jernkiste, står jo endnu i Rabba i Ammon, ni Alen lang og fire Alen bred efter vanligt Mål.
(Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
12 Således tog vi dengang dette Land i Besiddelse. Landet fra Aroer, der ligger ved Arnonfloden, og Halvdelen af Gileads Bjerge med Byerne der gav jeg Rubeniterne og Gaditerne;
Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
13 men Resten af Gilead og hele Basan, Ogs Rige, gav jeg til Manasses halve Stamme, hele Landskabet Argob. (Det er hele dette Basan, man kalder Refaiterland.)
Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
14 Manasses Søn Jair erobrede hele Landskabet Argob indtil Gesjuriternes og Ma'akatiternes Egne og kaldte dem Ja'irs Teltbyer efter sig selv, som de hedder endnu den Dag i Dag.
Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
15 Og Makir gav jeg Gilead;
Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
16 og Rubeniterne og Gaditerne gav jeg Landet fra Gilead til Arnonfloden med Dalens Midtlinie som Grænse og til Jabbokfloden, Ammoniternes Grænse,
Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
17 og Arabalavningen med Jordan som Grænse fra Kinneret til Arabaeller Salthavet ved Foden af Pisgas Skrænter mod Øst.
Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
18 Dengang gav jeg eder følgende Påbud: "HERREN eders Gud har givet eder dette Land i Eje; men I skal, så mange krigsdygtige Mænd I er, drage væbnede i Spidsen for eders Brødre Israelitterne
Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
19 kun eders Kvinder, Børn og Kvæg (jeg ved, at I har meget Kvæg) skal blive tilbage i de Byer, jeg giver eder
Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
20 indtil HERREN bringer eders Brødre til Hvile ligesom eder, og de også får taget det Land i Besiddelse, som HERREN eders Gud vil give dem hinsides Jordan; så kan enhver af eder vende tilbage til den Ejendom, jeg har givet eder!"
sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
21 Og Josua gav jeg dengang følgende Påbud: "Du har med egne Øjne set alt, hvad HERREN eders Gud har gjort ved disse to Konger; således vil HERREN også gøre ved alle de Riger, du drager over til.
A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
22 Du skal ikke frygte for dem; thi HERREN eders Gud vil selv kæmpe for eder!"
Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
23 Og dengang bad jeg således til HERREN:
A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
24 "Herre, HERRE! Du har begyndt at vise din Tjener din Storhed og din stærke Hånd! Thi hvem er den Gud i Himmelen og på Jorden, der kan gøre sådanne Gerninger og Storværker som du?
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
25 Lad mig da få Lov at drage over og se det herlige Land hinsides Jordan, det herlige Bjergland og Libanon!"
Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
26 Men HERREN var vred på mig for eders Skyld og hørte mig ikke, men han sagde til mig: "Lad det være nok, tal ikke mere til mig om den Sag;
Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
27 men stig op på Pisgas Tinde, løft dit Blik mod Vest og Nord, mod Syd og Øst, og tag det i Øjesyn. Thi du kommer ikke til at drage over Jordan dernede;
Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
28 men sig Josua, hvad han skal, og sæt Mod i ham og styrk ham, thi det bliver ham, der skal drage over i Spidsen for dette Folk, og ham, der skal give dem det Land, du ser, i Eje."
Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
29 Så blev vi i Dalen lige over for Bet Peor.
Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.