< 5 Mosebog 27 >

1 Derpå bød Moses og IsraeLs Ældste Folket: "Hold alle de Bud, jeg i Dag pålægger eder!
Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
2 Og den Dag I går over Jordan ind i det Land, HERREN din Gud vil give dig, skal du oprejse dig nogle store Sten og kalke dem over,
Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
3 og på dem skal du skrive alle denne Lovs Ord, så snart du er kommet over, for at du kan drage ind i det Land, HERREN din Gud vil give dig, et Land, der flyder med Mælk og Honning, som HERREN, dine Fædres Gud, lovede dig.
Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
4 Og når I er kommet over Jordan, skal I oprejse disse Sten, om hvilke jeg i Dag giver eder Pålæg, på Ebals Bjerg og kalke dem over.
Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
5 Og der skal du bygge HERREN din Gud et Alter, et Alter af Sten, som du ikke har svunget Jern over;
Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
6 af utilhugne Sten skal du bygge HERREN din Guds Alter, og på det skal du ofre Brændofre til HERREN din Gud,
Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
7 og du skal ofre Takofre og holde Måltid der og være glad for HERREN din Guds Åsyn.
Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
8 Og på Stenene skal du skrive alle denne Lovs Ord tydeligt og klart!"
Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
9 Derpå talte Moses og Levitpræsterne til hele Israel og sagde: "Hør efter i Stilhed, Israel! I Dag er du blevet HERREN din Guds Folk!
Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
10 Så lyt da til HERREN din Guds Røst og hold hans Bud og Anordninger, som jeg i Dag pålægger dig!"
Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
11 Og Moses bød på denne Da: Folket:
A wannan rana Musa ya umarce mutane,
12 "Når I er kommet over Jordan, skal den ene Del af eder tage Plads på Garizims Bjerg for at velsigne Folket, nemlig Simeon, Levi, Juda, Issakar, Josef og Benjamin;
Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
13 og den anden skal tage Plads på Ebals Bjerg for at forbande, nemlig Ruben, Gad, Aser, Zebulon, Dan og Naftali."
Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
14 Og Leviterne skal tage til Orde og med høj Røst sige til alle Israels Mænd:
Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
15 "Forbandet være den, som laver et udskåret eller støbt Billede, HERREN en Vederstyggelighed, Værk af en Håndværkers Hænder, og stiller det op i Løndom!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
16 "Forbandet enhver, som ringeagter sin Fader eller Moder!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
17 "Forbandet enhver, som flytter sin Næstes Skel!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
18 "Forbandet enhver, som fører den blinde på Vildspor!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
19 "Forbandet enhver, som bøjer Retten for den fremmede, den faderløse og Enken!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
20 "Forbandet enhver, som har Samleje med sin Faders Hustru; thi han har løftet sin Faders Tæppe!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
21 "Forbandet enhver, som har Omgang med noget Slags Kvæg!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
22 "Forbandet enhver, som har Samleje med sin Søster, sin Faders eller Moders Datter!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
23 "Forbandet enhver, som har Samleje med sin Hustrus Moder!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
24 "Forbandet enhver, som snigmyrder sin Næste!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
25 "Forbandet enhver, som lader sig købe til at myrde en uskyldig!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
26 "Forbandet enhver, som ikke holder denne Lovs Ord i Hævd og handler efter dem!" Og hele Folket skal svare: "Amen!"
“La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”

< 5 Mosebog 27 >