< 5 Mosebog 17 >

1 Du må ikke ofre HERREN din Gud en Okse eller et Stykke Småkvæg, som har nogen Lyde, nogen som helst Fejl; thi det er HERREN din Gud en Vederstyggelighed.
Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
2 Når der et steds i din Midte inden dine Porte, som HERREN din Gud vil give dig, findes nogen, Mand eller Kvinde, der gør, hvad der er ondt i HERREN din Guds Øjne, og overtræder hans Pagt,
In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
3 idet han går hen og dyrker andre Guder og tilbeder dem, Solen, Månen eller Himmelens hele Hær, hvad jeg ikke har pålagt eder,
wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
4 og det bliver dig meldt, så du får det af høre, da skal du omhyggeligt undersøge Sagen, og hvis det viser sig, at det virkelig forholder sig således, at der er øvet en sådan Vederstyggelighed i Israel,
in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
5 da skal du føre Manden eller Kvinden, som har øvet denne Udåd, ud til Byporten, hvad enten det nu er en Mand eller en Kvinde, og stene dem til Døde.
sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
6 På to eller tre Vidners Udsagn skal Dødsdommen udføres; den må ikke udføres på et enkelt Vidnes Udsagn.
Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
7 Vidnernes Hånd skal først løfte sig imod ham for at slå ham ihjel, siden alle de andres Hånd. Således skal du udrydde det onde af din Midte.
Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
8 Når en Retssag angående Blodsudgydelse eller et Ejendomsspørgsmål eller Legemsskade, når i det hele en eller anden Retstrætte inden dine Porte er dig for vanskelig, skal du stå op og drage til det Sted, HERREN din Gud udvælger,
In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
9 og henvende dig til Levitpræsterne og den Dommer, som er der til den Tid, og spørge dem til Råds, så skal de give dig til Hen, hvorledes der skal dømmes i Sagen.
Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
10 Og du skal rette dig efter den Afgørelse, de giver dig til kende fra det Sted, HERREN udvælger, og omhyggeligt handle efter alt det, som de lærer dig.
Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
11 Efter den Vejledning, de giver dig, og efter den Kendelse, de kundgør dig, skal du handle uden at vige til højre eller venstre fra, hvad de giver dig til Kende.
Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
12 Og den Mand, der formaster sig til ikke at lyde Præsten, som gør Tjeneste der for HERREN din Gud, eller Dommeren, den Mand skal dø, og du skal udrydde det onde af Israel.
Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
13 Og det skal høres i hele Folket, så de gribes af Frygt og ikke mere handler formasteligt.
Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
14 Når du kommer ind i det Land, HERREN din Gud vil give dig, og får taget det i Besiddelse og fæstet Bo der, og du så får den Tanke, at du vil have en Konge over dig ligesom alle de andre Folk rundt om dig,
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
15 så må du kun sætte den Mand til Konge over dig, som HERREN din Gud udvælger. Af dine Brødres Midte skal du tage dig en konge. En fremmed, der ikke hører til dine Brødre, må du ikke tage til konge over dig.
ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
16 Kun må han ikke holde mange Heste og sende Folket tilbage til Ægypten for at skaffe sig mange Heste; thi HERREN har jo sagt til eder: "I må ikke mere vende tilbage ad den Vej!"
Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
17 Heller ikke må han have mange Hustruer, for at hans Hjerte ikke skal forledes til Frafald, og han må ikke samle sig Sølv og Guld i Overflod.
Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
18 Når han så har sat sig på Tronen, skal han skaffe sig en Afskrift af denne Lov hos Levitpræsterne;
Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
19 og han skal have den hos sig og læse i den alle sine Levedage, at han kan lære at frygte HERREN sin Gud, så han tager Vare på alle denne Lovs Ord og på disse Anordninger og holder dem,
Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
20 for at hans Hjerte ikke skal hovmode sig over hans Brødre eller vige til højre eller venstre fra Budet, at han og hans Sønner i lange Tider må have Kongemagten i Israel.
don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.

< 5 Mosebog 17 >