< Daniel 8 >

1 I Kong Belsazzars tredje regeringsår viste der sig et syn for mig, Daniel; det kom efter det, som tidligere havde vist sig for mig.
A shekara ta uku ta mulkin sarki Belshazar, ni, Daniyel, na ga wahayi, bayan wancan da na riga gani.
2 Jeg skuede i Synet, og det var mig, som om jeg var i Borgen Susan i Landskabet Elam; og jeg så mig i Synet stående ved Floden Ulaj.
A cikin wahayin, na ga kaina a mafakar Shusha a yankin Elam; a wahayin na ga ina a bakin Kogin Ulai.
3 Da løftede jeg mine Øjne og skuede, og se, en Væder stod ved Floden; den havde to store Horn, det ene større end det andet, og det største skød op sidst.
Na ɗaga ido, a gabana kuwa sai ga rago mai ƙahoni biyu, yana tsaye a gefen mashigin kogin, ƙahonin kuma suna da tsawo. Ɗaya daga cikin ƙahonin ya fi ɗayan tsawo. Wanda ya fi tsawon shi ne ya tsiro daga baya.
4 Jeg så Væderen stange mod Vest, Nord og Syd; intet Dyr kunde modstå den, ingen kunde redde af dens Vold, og den gjorde, hvad den vilde, og blev mægtig.
Na lura da ragon sa’ad da ya kai karo wajen yamma da arewa da kudu. Babu wata dabbar da ta iya ƙarawa da shi, babu kuma wanda ya iya kuɓuta daga ikonsa. Ya yi yadda ya ga dama, ya kuma zama mai girma.
5 Videre så jeg nøje til, og se, en Gedebuk kom fra Vest farende hen over hele Jorden, men uden at røre den; og Bukken havde et anseligt Horn i Panden.
Yayinda nake tunani game da wannan, farat ɗaya sai ga bunsurun da yake da sanannen ƙaho tsakanin idanunsa ya ɓullo daga wajen yamma, yana ratsa dukan duniya ba ya ko taɓa ƙasa.
6 Den kom hen til den tvehornede Væder, som jeg havde set stå ved Floden, og løb imod den med ubændig Kraft;
Ya zo wajen rago mai ƙahoni biyu ɗin nan da na riga na gani tsaye a gefen mashigin kogin nan ya tasar masa da fushi mai zafi.
7 og jeg så, hvorledes den, da den nåede Væderen, rasende stormede imod den, stødte til den og sønderbrød begge dens Horn; og Væderen havde ikke kraft til at modstå den, men Bukken kastede den til Jorden og trampede på den, og ingen reddede Væderen af dens Vold.
Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, ya kai wa ragon hari. Ya kakkarya ƙahoninsa nan biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, bai iya kāre kansa daga bunsurun ba. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun.
8 Derpå blev Gedebukken såre mægtig; men som den var allermægtigst, brødes det store Horn af, og i Stedet voksede fire andre frem mod alle fire Verdenshjørner.
Bunsurun kuwa ya ƙasaita, amma a ƙwanƙolin ikonsa sai aka karye babban ƙahonsa, kuma a wurin da ƙahon nan ya kasance waɗansu sanannun ƙahoni huɗu suka tsiro suna fuskantar kusurwoyin nan huɗu.
9 Men fra det ene af dem skød et andet og lille Horn op, og det voksede umådeligt mod Syd og Øst og mod det herlige Land;
Daga cikin ɗayansu kuma wani ƙaramin ƙaho ya fito, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai zuwa kudu da kuma gabas da wajen Kyakkyawar Ƙasa.
10 og det voksede helt op til Himmelens Hær, styrtede nogle af Hæren og af Stjernerne til Jorden og trampede på dem.
Ya yi girma sai da ya kai rundunar sammai, ya kuma fid da waɗansu rundunar taurari zuwa ƙasa ya kuma tattake su.
11 Og det hovmodede sig mod Hærens Øverste; hans daglige Offer blev ophævet, og hans Helligdoms Sted kastedes til Jorden.
Sai ya ɗora kansa ya zama mai girma kamar Sarkin runduna; sai aka ɗauke hadaya ta kullayaumi daga gare shi, aka kuma saukar da wurin masujadarsa ƙasa.
12 Og på Alteret for det daglige Offer lagdes en Misgerning; Sandheden kastedes til Jorden, og Hornet havde Lykke med, hvad det gjorde.
Saboda tawaye, sai aka ba da rundunar tsarkaka da kuma hadayar ƙonawa ta kowace rana ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara.
13 Da hørte jeg en hellig tale, og en anden hellig spurgte den talende: "Hvor lang Tid gælder Synet om, at det daglige Offer ophæves, Ødelæggelsens Misgerning opstilles, og Helligdommen og Hæren nedtrampes?"
Sa’an nan na ji mai tsarkin nan yana magana, wani mai tsarki kuma ya ce da wancan, “Har yaushe wannan wahayi zai tabbata, wahayi game da hadaya ta kullayaumi, da tawayen da yake kawo lalacewa, da kuma miƙa wuri mai tsarki da kuma na rundunar da za a tattake a ƙarƙashin sawu?”
14 Han svarede: "2300 Aftener og Morgener; så skal Helligdommen komme til sin Ret igen!"
Sai ya ce mini, “Zai ɗauki safiya da yamma 2,300; sa’an nan za a sāke tsarkake wuri mai tsarki.”
15 Medens jeg, Daniel, nu så Synet og søgte at forstå det, se, da stod der for mig en som en Mand at se til,
Yayinda ni, Daniyel, nake duban wahayi ina ƙoƙari in fahimce shi, sai ga wani a gabana wanda ya yi kama da mutum.
16 og jeg hørte en menneskelig Røst råbe over Ulaj: "Gabriel, udlæg ham Synet!"
Sai na ji muryar wani mutum daga Ulai tana cewa, “Jibra’ilu, faɗa wa wannan mutum ma’anar wahayin.”
17 Så kom han hen, hvor jeg stod, og ved hans Komme blev jeg overvældet af Rædsel og faldt på mit Ansigt. Og han sagde til mig: "Se nøje til, Menneskesøn, thi Synet gælder Endens Tid!"
Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
18 Medens han taledemed mig, lå jeg bedøvet med Ansigtet mod Jorden; men han rørte ved mig og fik mig på Benene
Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
19 og sagde: "Se, jeg vil kundgøre dig, hvad der skal ske i Vredens sidste Tid; thi Synet gælder Endens bestemte Tid.
Sai ya ce, “Zan faɗa maka abin da zai faru a lokacin fushi, saboda wahayin yana magana ne a kan lokacin da aka ƙayyade na ƙarshe.
20 Den tvehornede Væder, du så, er Kongerne af Medien og Persien,
Rago mai ƙahoni biyu da ka gani, yana a madadin sarakunan Medes da Farisa ne.
21 den lådne Buk er Kongen af Grækenland, og det store Horn i dens Pande er den første Konge.
Bunsurun kuwa sarkin Girka ne, kuma babban ƙahon da yake tsakanin idanunsa, sarki na farko ne.
22 At det brødes af, og at fire andre voksede frem i Stedet, betyder, at fire Riger skal fremstå af hans Folk, dog uden hans Kraft.
Ƙahoni huɗu da suka maya wannan da ya karye yana a madadin masarautu huɗu da za su tashi daga cikin al’ummarsa amma ba za su sami irin ikonsa ba.
23 Men i deres Herredømmes sidste Tid, når Overtrædelserne har gjort Målet fuldt, skal en fræk og rænkefuld konge fremstå.
“Can wajen ƙarshe mulkinsu, sa’ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai rashin hankali, uban makirci, zai fito.
24 Hans Magt skal blive stor, dog ikke som hins; han skal tale utrolige Ting og have Lykke med, hvad han gør, og gennemføre sine Råd og ødelægge mægtige Mænd.
Zai yi ƙarfi ƙwarai da gaske, amma ba da ikonsa ba. Zai jawo mummunar hallakarwa kuma zai yi nasara a duk abin da ya sa gaba. Zai hallakar da majiya ƙarfi da kuma tsarkaka.
25 Mod de hellige skal hans Tanke rettes; hans svigefulde Råd skal lykkes ham, og han skal sætte sig store Ting for og styrte mange i Ulykke i deres Tryghed. Mod Fyrsternes Fyrste skal han rejse sig, men så skal han knuses, dog ikke ved Menneskehånd.
Zai sa yaudara ta ƙara yin yawa, zai ɗaukaka kansa. Sa’ad da suke ji sun sami mafaka, zai hallaka mutane da yawa sa’an nan kuma yă fara gāba da Sarkin sarakuna. Duk da haka za a hallaka shi, amma ba da ikon mutum ba.
26 Synet om Affenerne og Morgenerne, hvorom der var Tale, er Sandhed. Men du skal lukke for Synet; thi det gælder en fjern Fremtid."
“Wahayin nan na safiya da yamma da aka nuna maka gaskiya ne, amma ka ɓoye wahayin, gama ya shafi nan gaba mai tsawo ne.”
27 Men jeg, Daniel, lå syg en Tid lang; så stod jeg op og udførte min Gerning i kongens Tjeneste. Jeg var rædselslagen over Synet og forstod det ikke.
Ni, Daniyel, na gaji matuƙa na kuma yi rashin lafiya na kwanaki masu yawa. Sa’an nan sai na tashi na ci gaba da hidimar sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ya fi ƙarfin fahimtata.

< Daniel 8 >