< Daniel 5 >

1 Kong Belsazzar gjorde et stort gæstebud for sine tusinde Stormænd og drak Vin med dem.
Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
2 Og påvirket af Vinen lod han de Guldkar og Sølvkar hente, som hans Fader Nebukadnezar havde ført bort fra Helligdommen i Jerusalem, for at Kongen og hans Stormænd, hans Hustruer og Medhustruer kunde drikke af dem.
Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
3 Man hentede da Guld og Sølvkarrene, som var ført bort fra Helligdommen, Guds Hus i Jerusalem, og Kongen og hans Stormænd, hans Hustruer og Medhustruer drak af dem;
Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
4 og medens de drak Vin, priste de deres Guder af Guld, Sølv, Kobber, Jern, Træ og Sten.
Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
5 Men i samme Stund viste der sig Fingre af en Menneskehånd, som skrev på Væggens Kalk i Kongens Palads over for Lysestagen, og Kongen så Hånden, som skrev.
Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
6 Da skiftede Kongen Farve, hans Tanker forfærdede ham, hans Hofters Ledemod slappedes, og hans Knæ slog imod hinanden.
Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
7 Og kongen råbte med høj Røst, at man skulde føre Manerne, Kaldæerne og Stjernetyderne ind; og Kongen tog til Orde og sagde til Babels Vismænd: "Enhver, som kan læse denne Skrift og tyde mig den, skal klædes i Purpur, Guldkæden skal hænges om hans Hals, og han skal være den tredje mægtigste i Riget."
Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
8 Så kom alle Babels Vismænd til Stede, men de evnede hverken at læse Skriften eller tyde den for Kongen.
Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
9 Da blev Kong Belsazzar højlig forfærdet, og han skiftede Farve: også hans Stormænd stod rædselslagne.
Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
10 Ved Kongens og hans Stormænds Råb kom Dronningen ind i Gildesalen, og hun tog til Orde og sagde: "Kongen leve evindelig! Lad ikke dine Tanker forfærde dig og skift ikke Farve!
Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
11 I dit Rige findes en Mand, i hvem hellige Guders Ånd er, og som i din Faders Dage fandtes at sidde inde med Viden, Indsigt og en Visdom som selve Guderne, så din Fader Nebukadnezar satte ham til Øverste for Drømmetyderne, Manerne, Kaldæerne og Stjernetyderne,
Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
12 eftersom en ypperlig Ånd, Kundskab og Indsigt til at udtyde Drømme, råde Gåder og løse Knuder fandtes hos denne Daniel, hvem kongen gav Navnet Beltsazzar. Lad derfor Daniel kalde, at han kan tyde det!"
Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
13 Så førtes Daniel ind for Kongen. Og Kongen tog til Orde og sagde til ham: "Er du Daniel, en af de fangne Judæere, som min Fader Kongen bortførte fra Juda?
Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
14 Jeg har hørt om dig, at Guders Ånd er i dig, og at du er fundet at sidde inde med Viden, Kløgt og ypperlig Visdom.
Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
15 Nu har Vismændene og Manerne været ført ind for mig for at læse denne Skrift og tyde mig den; men de evner ikke at tyde mig dette.
An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
16 Men jeg har hørt om dig, at du kan tyde Drømme og løse Knuder. Nu vel! Hvis du kan læse Skriften og tyde mig den, skal du klædes i Purpur, Guldkæden skal hænges om din Hals, og du skal være den tredje mægtigste i Riget."
Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
17 Så svarede Daniel Kongen: "Spar dine Gaver og giv en anden dine Foræringer! Men Skriften vil jeg læse og tyde for Kongen.
Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
18 Den højeste Gud, o Konge, gav din Fader Nebukadnezar Kongedømme, Magt, Herlighed og Ære;
“Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
19 og for den Storheds Skyld, som han havde givet ham, frygtede og bævede alle Folk, Stammer og Tungemål for ham; han dræbte, hvem han vilde, og lod leve, hvem han vilde; han ophøjede, hvem han vilde, og nedbøjede, hvem han vilde.
Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
20 Men da hans Hjerte blev hovmodigt og hans Ånd stolt og overmodig, stødtes han fra Kongetronen, og hans Herlighed fratoges ham.
Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
21 Af Menneskenes Samfund blev han udstødt, og hans Hjerte blev som et Dyrs; han boede hos Vildæslerne, han måtte æde Græs som Kvæget, og af Himmelens Dug vædedes hans Legeme, til han skønnede, at den højeste Gud er Herre over Menneskenes Rige og kan ophøje, hvem han vil, til Hersker derover.
Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
22 Men du, Belsazzar, hans Søn, har ikke ydmyget dit Hjerte, skønt du vidste alt dette;
“Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
23 du har hovmodet dig mod Himmelens Herre! Hans Huses Kar har man hentet til dig, og du og dine Stormænd, dine Hustruer og Medhustruer drak Vin af dem; og du priste dine Guder af Sølv, Guld, Kobber, Jern, Træ og Sten, som hverken kan se eller høre eller fatte; men den Gud, som holder din Livsånde i sin Hånd og råder over alle dine Veje, ham ærede du ikke.
A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
24 Derfor er denne Hånd udsendt fra ham og Skriften der optegnet.
Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
25 Og således lyder Skriften: Mené, mené, tekél ufarsin!
“Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
26 Og Ordene skal tydes således: Mené betyder: Gud har talt dit Riges Dage og gjort Ende derpå.
“Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
27 Tekél betyder: Du er vejet på Vægten og fundet for let.
“Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
28 Perés betyder: Dit Rige er delt og givet til Medien og Persien."
“Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
29 Så blev Daniel på Belsazzars Bud klædt i Purpur, Guldkæden hængtes om hans Hals, og man udråbte, at han skulde være den tredje mægtigste i Riget.
Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
30 Men samme Nat blev Belsazzar, Kaldæernes Konge, dræbt,
A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
31 og Mederen Darius overtog Riget i en Alder af to og tresindstyve År.
Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.

< Daniel 5 >