< Daniel 11 >
1 der står som Hjælp og Støtte for mig. Dog vil jeg nu kundgøre dig, hvad der står skrevet i Sandhedens Bog;
A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
2 ja, nu vil jeg kundgøre dig, hvad sandt er. Se, endnu skal der fremstå tre konger i Persien, og den fjerde skal komme til større Rigdom end nogen af de andre; og når han er blevet mægtig ved sin Rigdom, skal han opbyde alt imod det græske Rige.
“Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
3 Men da fremstår en Heltekonge, og han skal råde med Vælde og gøre, hvad han vil.
Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
4 Men bedst som han står, skal hans Rige sprænges og deles efter de fire Verdenshjørner, og det skal ikke tilfalde hans Efterkommere eller blive så mægtigt, som da han rådede, men hans Rige skal ødelægges og gå over til andre end Efterkommerne.
Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
5 Siden bliver Sydens konge mægtig, men en af hans Fyrster bliver stærkere end han og får Magten; og hans Magt skal blive stor.
“Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
6 Men nogle År senere slutter de Forbund, og Sydens Konges Datter drager ind til Nordens Konge for at tilvejebringe Fred; men Armens Kraft holder ikke Stand, hans Arm holder ikke ud, men hun gives i Døden tillige med sit Følge, sin Søn og sin Ægtemand.
Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
7 I de Tider skyder der i hans Sted et Skud frem af hendes Rødder; og han drager mod Nordens konges Hær og trænger ind i hans Fæstning, fuldbyrder sin Vilje på dem og bliver mægtig,
“Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
8 endog deres Guder med deres støbte Billeder og deres kostbare Kar, Sølv og Guld, fører han med som Bytte til Ægypten; siden skal han en Tid lang lade Nordens Konge i Ro.
Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
9 Men denne falder ind i Sydens Konges Rige; dog må han vende hjem til sit Land.
Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
10 Men hans Søn ruster sig og samler store Hære i Mængde, drager frem imod ham og oversvømmer og overskyller Landet. Og han kommer igen og trænger frem til hans Fæstning.
’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
11 Men Sydens konge bliver rasende og rykker ud til Kamp imod Nordens Konge; han stiller en stor Hær på Benene, men den gives i Sydens Konges Hånd.
“Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
12 Når Hæren er oprevet, bliver hans Hjerte stolt; han strækker Titusinder til Jorden, men hævder ikke sin Magt.
Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
13 Nordens Konge stiller på ny en Hær på Benene, større end den forrige, og nogle År senere drager han imod ham med en stor Hær og et vældigt Tros.
Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
14 Og i de Tiderer der mange, som gør Oprør imod Sydens Konge. og Voldsmændene i dit Folk rejser sig, for at Åbenbaringen kan gå i Opfyldelse, men selv falder de.
“A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
15 Nordens Konge rykker frem, opkaster Volde og indtager en Fæstning; og Sydens Arme skal ikke holde ud; hans Hær flygter og har ikke Modstands kraft.
Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
16 Den, som rykker imod ham, gør, hvad han vil, og ingen står sig imod ham; han sætter sig fast i det herlige Land og bringer Ødelæggelse med sig.
Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
17 Han oplægger Råd om at komme med hele sit Riges Styrke, men slutter Fred med ham og giver ham sin Datter til Ægte til Landets Ulykke; men det bliver ikke til noget og lykkes ikke for ham.
Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
18 Så vender han sig mod Kystlandene og indtager mange, men en Hærfører gør Ende på hans Hån; syv Fold gengælder han ham hans Hån.
Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
19 Derpå vender han sig mod sit eget Lands Fæstninger, men han snubler, falder og forsvinder.
Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
20 I hans Sted træder en, som sender en Skatteopkræver gennem Rigets Herlighed, men på nogle Dage knuses han, dog uden Harm, ej heller i Strid.
“Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
21 I hans Sted træder en Usling. Kongedømmets Herlighed overdrages ham ikke, men han kommer, før nogen aner Uråd, og tilriver sig Kongedømmet ved Rænker.
“Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
22 Hære bortskylles helt foran ham, også en Pagtsfyrste knuses.
Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
23 Så snart man har sluttet Forbund med ham, øver han Svig; han drager frem og bliver stærk ved en Håndfuld Folk.
Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
24 Uventet falder han ind i de frugtbareste Egne og gør, hvad hans Fædre eller Fædres Fædre ikke gjorde; Ran, Bytte og Gods strør han ud til sine Folk, og mod Fæstninger oplægger han Råd, dog kun til en Tid.
Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
25 Han opbyder sin kraft og sit Mod mod Sydens Konge og drager ud med en stor Hær; og Sydens Konge rykker ud til Strid med en overmåde stor og stærk Hær, men kan ikke stå sig, da der smedes Rænker imod ham;
“Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
26 hans Bordfæller bryder hans Magt, hans Hær skylles bort, og mange dræbes og falder.
Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
27 Begge Konger har ondt i Sinde og sidder til Bords sammen og lyver; men det lykkes ikke, thi Enden tøver endnu til den fastsatte Tid.
Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
28 Da han er på Hjemvejen til sit Land med store Forråd, oplægger hans Hjerte Håd mod den hellige Pagt, og han fuldfører det og vender hjem til sit Land.
“Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
29 Til den fastsatte Tid drager han atter mod Syd, men det går ikke anden Gang som første;
“A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
30 kittæiske Skibe drager imod ham, og han lader sig skræmme og vender om; hans Vrede blusser op mod den hellige Pagt, og han giver den frit Løb. Så vender han hjem og mærker sig dem, som falder fra den hellige Pagt.
Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
31 Og hans Hære skal stå der og vanhellige Helligdommen, den faste Borg, afskaffe det daglige Offer og rejse Ødelæggelsens Vederstyggelighed.
“Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
32 Dem, der overtræder Pagten, lokker han ved Smiger til Frafald; men de Folk, som kender deres Gud, står fast og viser det i Gerning.
Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
33 De kloge i Folket skal bringe mange til Indsigt, men en Tid lang bukker de under for Ild og Sværd, Fangenskab og Plyndring.
“Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
34 Medens de bukker under, får de en ringe Hjælp, og mange slutter sig til dem på Skrømt.
Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
35 Af de kloge må nogle bukke under, for at der kan renses ud iblandt dem, så de sigtes og renses til Endens Tid; thi endnu tøver den til den bestemte Tid.
Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
36 Og Kongen gør, hvad han vil, ophøjer og hovmoder sig mod enhver Gud; mod Gudernes Gud taler han utrolige Ting, og han har Lykken med sig, indtil Vreden er omme; thi hvad der er besluttet, det sker.
“Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
37 Sine Fædres Guder ænser han ikke; ej heller ænser han Kvindernes Yndlingsgud eller nogen anden Gud, men hovmoder sig mod dem alle.
Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
38 I Stedet ærer han Fæstningernes Gud; en Gud, hans Fædre ikke kendte, ærer han med Guld, Sølv, Ædelsten og Klenodier.
A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
39 I de faste Borge lægger han den fremmede Guds Folk; dem, der vedkender sig ham, overøser han med Ære og giver dem Magt over mange, og han uddeler Land til Løn.
Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
40 Men ved Endens Tid skal Sydens Konge prøve Kræfter med ham, og Nordens Konge stormer imod ham med Vogne, Ryttere og Skibe i Mængde og falder ind i Landene, oversvømmer og overskyller dem.
“A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
41 Han falder ind i det herlige Land, og Titusinder falder; men følgende skal reddes af hans Bånd: Edom, Moab og en Levning Ammoniter.
Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
42 Han udrækker sin Hånd mod Landene, og Ægypten undslipper ikke.
Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
43 Han bliver Herre over Guld og Sølvskattene og alle Ægyptens Klenodier; der er Libyere og Ætiopere i hans Følge.
Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
44 Men Rygter fra Øst og Nord forfærder ham, og han drager bort i stor Harme for at tilintetgøre mange og lægge Band på dem.
Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
45 Han opslår sine Paladstelte mellem Havet og det hellige, herlige Bjerg. Men han går sin Bane i Møde, og ingen kommer ham til Hjælp.
Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.