< Amos 8 >

1 Således lod Herren mig skue: Se, der var en kurv sommerfrugt.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
2 Og han sagde: "Hvad ser du, Amos?" Jeg svarede: "En kurv Sommerfrugt!" Da sagde HERREN til mig: "Enden er kommet for mit Folk Israel; jeg vil ikke længer bære over med det."
Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
3 Paladsets Sangerinder skal jamre på denne Dag, så lyder det fra den Herre HERREN. Dynger af Lig er henkastet alle Vegne.
“A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
4 Hør, I, som knuser de fattige, gør det af med de arme i Landet
Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
5 og siger: "Hvornår er Nymånen omme, så vi kan få solgt noget Korn, Sabbaten, så vi kan åbne vort Kornsalg, gøre Efaen lille og Sekelen stor og med Svig gøre Vægten falsk
Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
6 for at købe den ringe for Sølv, den fattige for et Par Sko og få Afaldskornet solgt?"
mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
7 HERREN svor ved Jakobs Stolthed: Aldrig glemmer jeg een af deres Gerninger!
Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
8 Må Jorden ej skælve derover og enhver, som bor på den, sørge? Den stiger overalt som Nilen og synker som Ægyptens Flod.
“Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
9 På hin Dag lader jeg det ske, så lyder det fra den Herre HERREN, at Solen går ned ved Middag, og Jorden bliver mørk ved højlys Dag.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
10 Jeg vender eders Fester til Sorg og alle eders Sange til klage, lægger Sæk om alle Lænder, gør hvert et Hoved skaldet, bringer Sorg som over en enbåren, en bitter Dag til sidst.
Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
11 Se, Dage skal komme, lyder det fra den Herre HERREN, da jeg sender Hunger i Landet, ikke Hunger efter Brød, ikke Tørst efter Vand, men efter at høre HERRENs Ord.
“Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
12 Da vanker de fra Hav til Hav, flakker fra Nord til Øst for at søge HERRENs Ord, men finder det ej.
Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
13 Den Dag vansmægter af Tørst de fagre Jomfruer og unge Mænd,
“A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
14 som sværger ved Samarias Synd, som siger: "Ved din Gud, o Dan!" "Ved din Skytsgud, o Be'ersjeba!" de skal falde, ej mere stå op.
Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”

< Amos 8 >