< Amos 5 >

1 Hør dette Ord, en klagesang, som jeg istemmer over eder, Israels Hus:
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 Hun er faldet og rejser sig ikke, Israels Jomfru, henstrakt på sin Jord, og ingen rejser hende op.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 Thi så siger den Herre HERREN: Den By, som går i Leding med tusind, får hundred tilbage, og den som går i Leding med hundred, får ti tilbage i Israels Hus.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 Thi så siger HERREN til Israels Hus: Søg mig, så skal I leve!
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 Søg ikke til Betel, gå ikke til Gilgal, drag ikke til Beersjeba! Thi Gilgal skal blive landflygtig, og Betel skal blive til intet.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Søg HERREN, så skal I leve, at ikke en Lue slår ud, en ædende Ild mod Josefs Hus, og Betel har ingen, som slukker.
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 Ve dem, som gør Ret til Malurt og kaster Retfærd i Støvet!
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 Syvstjernens og Orions Skaber, han, som vender Mulm til Morgen og gør Dag til Nattemørke, som kalder ad Havets Vande og gyder dem ud over Jorden, HERREN er hans Navn!
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 Han lader Ødelæggelse bryde ind over Borge, Ødelæggelse komme over Fæstninger.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 De hader Rettens Talsmand i Porten og afskyr den, som taler sandt.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Derfor, da I træder på den ringe og tager Afgift af hans Korn, skal I vel bygge Kvaderstenshuse, men ikke bo den; I skal vel plante yndige Vingårde, men Vinen skal I ikke drikke.
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 Jeg ved, eders Overtrædelser er mange og uden Tal eders Synder, I Rettens Fjender, som tager mod Bøde og bortviser fattige i Porten.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 Derfor tier den kloge i denne Tid, thi det er onde Tider.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Søg det gode, ej det onde, for at I må leve og Hærskarers Gud, må være med eder, som I siger, han er.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Had det onde og elsk det gode, hold Retten i Hævd i Porten! Måske vil da HERREN, Hærskarers Gud, være nådig mod Josefs Rest.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 Derfor, så siger HERREN, Herren, Hærskarers Gud: På alle Torve skal klages, i alle Gader råbes: "Ve! Ve!" Bonden kalder til Sorg, til Ligklage Klagemænd;
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 i hver en Vingård skal klages, når jeg drager igennem din Midte, siger HERREN.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Ve eder, som længes efter HERRENs Dag! Hvad vil I med HERRENs Dag? Mørke er den, ej Lys.
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 Da går det, som når en Mand flyr for en Løve og møder en Bjørn og, når han tyr ind i Huset og støtter sin Hånd til Væggen, bides af en Slange.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Ja, HERRENs Dag er Mørke, ej Lys, Bælgmørke uden Solskin.
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 Jeg hader, forsmår eders Fester, er led ved eders festlige Samlinger,
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 om også I bringer mig Brændofre. Eders Afgrødeofre behager mig ej, eders Fedekvægs-Takofre ser jeg ej til.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Spar mig dog for eders larmende Sang, eders Harpeklang hører jeg ikke.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 Nej, Ret skal vælde frem som Vand og Retfærd som svulmende Bæk.
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Bragte I mig Slagtoffer og Afgrødeoffer de fyrretyve Ørkenår, Israels Hus?
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 Så skal I da bære Sakkut, eders Konge, og Kevan, eders Gudestjerne, Billeder, som I har lavet eder.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 I Landflygtighed jager jeg eder hinsides Damaskus, siger HERREN; Hærskarers Gud er hans Navn.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.

< Amos 5 >