< Apostelenes gerninger 7 >

1 Men Ypperstepræsten sagde: "Forholder dette sig således?"
Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
2 Men han sagde: "I Mænd, Brødre og Fædre, hører til! Herlighedens Gud viste sig for vor Fader Abraham, da han var i Mesopotamien, førend han tog Bolig i Karan.
Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
3 Og han sagde til ham: "Gå ud af dit Land og fra din Slægt, og kom til det Land, som jeg vil vise dig."
Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
4 Da gik han ud fra Kaldæernes Land og tog Bolig i Karan; og efter hans Faders Død lod Gud ham flytte derfra hen i dette Land, hvor I nu bo.
“Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
5 Og han gav ham ikke Ejendom deri, end ikke en Fodsbred; dog forjættede han ham at give ham det til Eje og hans Sæd efter ham, endskønt han intet Barn havde.
Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
6 Men Gud talte således: "Hans Sæd skal være Udlændinge i et fremmed Land, og man skal gøre dem til Trælle og handle ilde med dem i fire Hundrede År.
Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
7 Og det Folk, for hvilket de skulle trælle, vil jeg dømme, sagde Gud; og derefter skulle de drage ud og tjene mig på dette Sted."
Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
8 Og han gav ham Omskærelsens Pagt. Og så avlede han Isak og omskar ham den ottende Dag, og Isak avlede Jakob, og Jakob de tolv Patriarker.
Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
9 Og Patriarkerne bare Avind imod Josef og solgte ham til Ægypten; og Gud var med ham,
“Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
10 og han udfriede ham af alle hans Trængsler og gav ham Nåde og Visdom for Farao, Kongen i Ægypten, som satte ham til Øverste over Ægypten og over hele sit Hus.
ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
11 Men der kom Hungersnød over hele Ægypten og Kanån og en stor Trængsel, og vore Fædre fandt ikke Føde.
“Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
12 Men da Jakob hørte, at der var Korn i Ægypten, sendte han vore Fædre ud første Gang.
Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
13 Og anden Gang blev Josef genkendt af sine Brødre, og Josefs Herkomst blev åbenbar for Farao.
A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
14 Men Josef sendte Bud og lod sin Fader Jakob og al sin Slægt kalde til sig, fem og halvfjerdsindstyve Sjæle.
Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
15 Og Jakob drog ned til Ægypten. Og han og vore Fædre døde,
Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
16 og de bleve flyttede til Sikem og lagte i den Grav, som Abraham havde købt for en Sum Penge af Hemors Sønner i Sikem.
Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
17 Som nu Tiden nærmede sig for den Forjættelse, Gud havde tilsagt Abraham, voksede Folket og formeredes i Ægypten,
“Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
18 indtil der fremstod en anden Konge, som ikke kendte Josef.
Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
19 Han viste Træskhed imod vor Slægt og handlede ilde med vore Fædre, så de måtte sætte deres små Børn ud, for at de ikke skulde holdes i Live.
Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
20 På den Tid blev Moses født, og han var dejlig for Gud; han blev opfostret i tre Måneder i sin Faders Hus.
“A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
21 Men da han var sat ud, tog Faraos Datter ham op og opfostrede ham til sin Søn.
Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
22 Og Moses blev oplært i al Ægypternes Visdom; og han var mægtig i sine Ord og Gerninger.
Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
23 Men da han blev fyrretyve År gammel, fik han i Sinde at besøge sine Brødre, Israels Børn.
“Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
24 Og da han så en lide Uret, forsvarede han ham og hævnede den mishandlede, idet han slog Ægypteren ihjel.
Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
25 Men han mente, at hans Brødre forstode, at Gud gav dem Frelse ved hans Hånd; men de forstode det ikke.
Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
26 Og den næste Dag viste han sig iblandt dem under en Strid og vilde forlige dem til at holde Fred, sigende: "I Mænd! I ere Brødre, hvorfor gøre I hinanden Uret?"
Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
27 Men den, som gjorde sin Næste Uret, stødte ham fra sig og sagde: "Hvem har sat dig til Hersker og Dommer over os?
“Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
28 Vil du slå mig ihjel, ligesom du i Går slog Ægypteren ihjel?"
Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
29 Da flygtede Moses for denne Tales Skyld og boede som fremmed i Midians Land, hvor han avlede to Sønner.
Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
30 Og efter fyrretyve Års Forløb viste en Engel sig for ham i Sinai Bjergs Ørken i en Tornebusk, der stod i lys Lue.
“Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
31 Men da Moses så det, undrede han sig over Synet, og da han gik hen for at betragte det, lød Herrens Røst til ham:
Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
32 "Jeg er dine Fædres Gud, Abrahams og Isaks og Jakobs Gud." Da bævede Moses og turde ikke se derhen.
‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
33 Men Herren sagde til ham: "Løs Skoene af dine Fødder; thi det Sted, som du står på, er hellig Jord.
“Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
34 Jeg har grant set mit Folks Mishandling i Ægypten og hørt deres Suk, og jeg er stegen ned for at udfri dem; og nu kom, lad mig sende dig til Ægypten!"
Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
35 Denne Moses, hvem de fornægtede, idet de sagde: "Hvem har sat dig til Hersker og Dommer," ham har Gud sendt til at være både Hersker og Befrier ved den Engels Hånd, som viste sig for ham i Tornebusken.
“Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
36 Ham var det, som førte dem ud, idet han gjorde Undere og Tegn i Ægyptens Land og i det røde Hav og i Ørkenen i fyrretyve År.
Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
37 Han er den Moses, som sagde til Israels Børn: "En Profet skal Gud oprejse eder af eders Brødre ligesom mig."
“Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
38 Han er den, som i Menigheden i Ørkenen færdedes med Engelen, der talte til ham på Sinai Bjerg, og med vore Fædre; den, som modtog levende Ord at give os;
Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
39 hvem vore Fædre ikke vilde adlyde, men de stødte ham fra sig og vendte sig med deres Hjerter til Ægypten, idet de sagde til Aron:
“Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
40 "Gør os Guder, som kunne gå foran os; thi vi vide ikke, hvad der er sket med denne Moses, som førte os ud af Ægyptens Land."
Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
41 Og de gjorde en Kalv i de Dage og bragte Offer til Gudebilledet og frydede sig ved deres Hænders Gerninger.
A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
42 Men Gud vendte sig fra dem og gav dem hen til at tjene Himmelens Hær, som der er skrevet i Profeternes Bog: "Have I vel, Israels Hus! bragt mig Slagtofre og andre Ofre i fyrretyve År i Ørkenen?
Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
43 Og I bare Moloks Telt og Guden Remfans Stjerne, de Billeder, som I havde gjort for at tilbede dem; og jeg vil flytte eder bort hinsides Babylon."
Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
44 Vore Fædre i Ørkenen havde Vidnesbyrdets Tabernakel, således som han, der talte til Moses, havde befalet at gøre det efter det Forbillede, som han havde set.
“Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
45 Dette toge også vore Fædre i Arv og bragte det under Josva ind i Landet, som Hedningerne besade, hvilke Gud fordrev fra vore Fædres Åsyn indtil Davids Dage,
Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
46 som vandt Nåde for Gud og bad om at måtte finde en Bolig for Jakobs Gud.
wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
47 Men Salomon byggede ham et Hus.
Amma Solomon ne ya gina masa gida.
48 Dog, den Højeste bor ikke i Huse gjorte med Hænder, som Profeten siger:
“Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
49 "Himmelen er min Trone, og Jorden mine Fødders Skammel, hvad Hus ville I bygge mig? siger Herren, eller hvilket er min Hviles Sted?
“‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
50 Har ikke min Hånd gjort alt dette?"
Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
51 I hårde Halse og uomskårne på Hjerter og Øren! I stå altid den Helligånd imod; som eders Fædre, således også I.
“Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
52 Hvem af Profeterne er der, som eders Fædre ikke have forfulgt? og de ihjelsloge dem, som forud forkyndte om den retfærdiges Komme, hvis Forrædere og Mordere I nu ere blevne,
An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
53 I, som modtoge Loven under Engles Besørgelse og have ikke holdt den!"
ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
54 Men da de hørte dette, skar det dem i deres Hjerter, og de bede Tænderne sammen imod ham.
Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
55 Men som han var fuld af den Helligånd, stirrede han op imod Himmelen og så Guds Herlighed og Jesus stående ved Guds højre Hånd.
Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
56 Og han sagde: "Se, jeg ser Himlene åbnede og Menneskesønnen stående ved Guds højre Hånd."
Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
57 Men de råbte med høj Røst og holdt for deres Øren og stormede endrægtigt ind på ham.
Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
58 Og de stødte ham ud uden for Staden og stenede ham. Og Vidnerne lagde deres Klæder af ved en ung Mands Fødder, som hed Saulus.
Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
59 Og de stenede Stefanus, som bad og sagde: "Herre Jesus, tag imod min Ånd!"
Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
60 Men han faldt på Knæ og råbte med høj Røst: "Herre, tilregn dem ikke denne Synd!" Og som han sagde dette, sov han hen. (Kap.8) 1 Men Saulus fandt Behag i hans Mord.
Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.

< Apostelenes gerninger 7 >