< Apostelenes gerninger 22 >
1 " I Mænd, Brødre og Fædre! hører nu mit forsvar over for eder!"
“’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
2 Men da de hørte, at han talte til dem i det hebraiske Sprog, holdt de sig end mere stille. Og han siger:
Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
3 "Jeg er en jødisk Mand, født i Tarsus i Kilikien, men opfostret i denne Stad, oplært ved Gamaliels Fødder efter vor Fædrenelovs Strenghed og nidkær for Gud, ligesom I alle ere i Dag.
“Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
4 Og jeg forfulgte denne Vej indtil Døden, idet jeg lagde både Mænd og Kvinder i Lænker og overgav dem til Fængsler,
Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
5 som også Ypperstepræsten vidner med mig og hele Ældsterådet, fra hvem jeg endog fik Breve med til Brødrene i Damaskus og rejste derhen for også at føre dem, som vare der, bundne til Jerusalem, for at de måtte blive straffede.
kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
6 Men det skete, da jeg var undervejs og nærmede mig til Damaskus, at ved Middag et stærkt Lys fra Himmelen pludseligt omstrålede mig.
“Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
7 Og jeg faldt til Jorden og hørte en Røst, som sagde til mig: Saul! Saul! hvorfor forfølger du mig?
Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
8 Men jeg svarede: Hvem er du, Herre? Og han sagde til mig: Jeg er Jesus af Nazareth, som du forfølger.
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
9 Men de, som vare med mig, så vel Lyset, men hørte ikke hans Røst, som talte til mig.
Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
10 Men jeg sagde: Hvad skal jeg gøre, Herre? Men Herren sagde til mig: Stå op og gå til Damaskus; og der skal der blive talt til dig om alt, hvad der er bestemt, at du skal gøre.
“Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
11 Men da jeg havde mistet Synet ved Glansen af hint Lys, blev jeg ledet ved Hånden af dem, som vare med mig, og kom således ind i Damaskus.
Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
12 Men en vis Ananias, en Mand, gudfrygtig efter Loven, som havde godt Vidnesbyrd af alle Jøderne, som boede der,
“Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
13 kom til mig og stod for mig og sagde: Saul, Broder, se op! Og jeg så op på ham i samme Stund.
Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
14 Men han sagde: Vore Fædres Gud har udvalgt dig til at kende hans Villie og se den retfærdige og høre en Røst af hans Mund.
“Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
15 Thi du skal være ham et Vidne for alle Mennesker om de Ting, som du har set og hørt.
Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
16 Og nu, hvorfor tøver du? Stå op, lad dig døbe og dine Synder aftvætte, idet du påkalder hans Navn!
Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
17 Og det skete, da jeg var kommen tilbage til Jerusalem og bad i Helligdommen, at jeg faldt i Henrykkelse
“Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
18 og så ham, idet han sagde til mig: Skynd dig, og gå hastigt ud af Jerusalem, thi de skulle ikke af dig modtage Vidnesbyrd om mig.
na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
19 Og jeg sagde: Herre! de vide selv, at jeg fængslede og piskede trindt om i Synagogerne dem, som troede på dig,
“Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
20 og da dit Vidne Stefanus's Blod blev udgydt, stod også jeg hos og havde Behag deri og vogtede på deres Klæder, som sloge ham ihjel.
Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
21 Og han sagde til mig: Drag ud; thi jeg vil sende dig langt bort til Hedninger."
“Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
22 Men de hørte på ham indtil dette Ord, da opløftede de deres Røst og sagde: "Bort fra Jorden med en sådan! thi han bør ikke leve.""
Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
23 Men da de skrege og reve Klæderne af sig og kastede Støv op i Luften,
Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
24 befalede Krigsøversten, at han skulde føres ind i Borgen, og sagde, at man med Hudstrygning skulde forhøre ham, for at han kunde få at vide, af hvad Årsag de således råbte imod ham.
sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
25 Men da de havde udstrakt ham for Svøberne, sagde Paulus til den hosstående Høvedsmand: "Er det eder tilladt at hudstryge en romersk Mand, og det uden Dom?"
Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
26 Men da Høvedsmanden hørte dette, gik han til Krigsøversten og meldte ham det og sagde: "Hvad er det, du et ved at gøre? denne Mand er jo en Romer."
Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
27 Men Krigsøversten gik hen og sagde til ham: "Sig mig, er du en Romer?" Han sagde: "Ja."
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
28 Og Krigsøversten svarede: "Jeg har købt mig denne Borgerret for en stor Sum," Men Paulus sagde: "Jeg er endog født dertil."
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
29 Da trak de, som skulde til at forhøre ham, sig straks tilbage fra ham. Og da Krigsøversten fik at vide, at han var en Romer, blev også han bange, fordi han havde bundet ham.
Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
30 Men den næste Dag, da han vilde have noget pålideligt at vide om, hvad han anklagedes for af Jøderne, løste han ham og befalede, at Ypperstepræsterne og hele Rådet skulde komme sammen, og han førte Paulus ned og stillede ham for dem.
Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.