< Apostelenes gerninger 11 >

1 Men Apostlene og de Brødre, som vare rundt om i Judæa, hørte, at også Hedningerne havde modtaget Guds Ord.
Manzanni da’yan’uwa ko’ina a Yahudiya suka ji cewa Al’ummai ma sun karɓi maganar Allah.
2 Og da Peter kom op til Jerusalem, tvistedes de af Omskærelsen med ham og sagde:
Saboda haka sa’ad da Bitrus ya haura zuwa Urushalima, masu bin da suke da kaciya suka zarge shi
3 "Du er gået ind til uomskårne Mænd og har spist med dem."
suka ce, “Ka je gidan mutanen da suke marasa kaciya ka kuwa ci tare da su.”
4 Men Peter begyndte og forklarede dem det i Sammenhæng og sagde:
Bitrus ya fara yin musu bayani dalla-dalla yadda ya faru cewa,
5 "Jeg var i Byen Joppe og bad; og jeg så i en Henrykkelse et Syn, noget, der dalede ned, ligesom en stor Dug, der ved de fire Hjørner sænkedes ned fra Himmelen, og den kom lige hen til mig.
“Ina a birnin Yoffa ina addu’a, sai ga wahayi ya zo mini. Na ga ana sauko da wani abu kamar babban mayafi daga sama ta kusurwansa huɗu, ya kuma sauko inda nake.
6 Jeg stirrede på den og betragtede den og så da Jordens firføddede Dyr og vilde Dyr og krybende Dyr og Himmelens Fugle.
Na duba cikinsa na ga dabbobi masu ƙafa huɗu na duniya, da namun jeji, da masu ja da ciki, da kuma tsuntsayen sararin sama.
7 Og jeg hørte også en Røst, som sagde til mig: Stå op, Peter, slagt og spis!
Sa’an nan na ji wata murya tana ce mini, ‘Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.’
8 Men jeg sagde: Ingenlunde, Herre! thi aldrig kom noget vanhelligt eller urent i min Mund.
“Na amsa na ce, ‘Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.’
9 Men en Røst svarede anden Gang fra Himmelen: Hvad Gud har renset, holde du ikke for vanhelligt!
“Sai muryar daga sama ta yi magana sau na biyu, ta ce, ‘Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.’
10 Og dette skete tre Gange; så blev det igen alt sammen draget op til Himmelen.
Wannan ya faru har sau uku, sa’an nan duk aka sāke ɗauke shi zuwa sama.
11 Og se, i det samme stode tre Mænd ved det Hus, i hvilket jeg var, som vare udsendte til mig fra Kæsarea.
“Nan take sai ga mutum uku da aka aika wurina daga Kaisariya a tsaye a ƙofar gidan da nake.
12 Men Ånden sagde til mig, at jeg skulde gå med dem uden at gøre Forskel. Men også disse seks Brødre droge med mig, og vi gik ind i Mandens Hus.
Ruhu ya ce mini kada in yi wata-wata game da tafiya tare da su. Waɗannan’yan’uwa guda shida su ma suka rako ni, muka kuwa shiga gidan mutumin.
13 Og han fortalte os, hvorledes han havde set Engelen stå i hans Hus og sige: Send Bud til Joppe og lad Simon med Tilnavn Peter hente!
Ya kuma gaya mana yadda wani mala’ika ya bayyana a gidansa ya ce masa, ‘Ka aika zuwa Yoffa a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus.
14 Han skal tale Ord til dig, ved hvilke du og hele dit Hus skal frelses.
Zai kawo maka saƙo wanda ta wurinsa kai da dukan iyalinka za ku sami ceto.’
15 Men idet jeg begyndte at tale, faldt den Helligånd på dem ligesom også på os i Begyndelsen.
“Na fara magana ke nan, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu yadda ya sauko mana a farko.
16 Og jeg kom Herrens Ord i Hu, hvorledes han sagde: Johannes døbte med Vand, men I skulle døbes med den Helligånd.
Sa’an nan na tuna da abin da Ubangiji ya ce, ‘Yohanna ya yi baftisma da ruwa, amma za a yi muku baftisma daRuhu Mai Tsarki.’
17 Når altså Gud gav dem lige Gave med os, da de troede på den Herre Jesus Kristus, hvem var da jeg, at jeg skulde kunne hindre Gud?"
To, in Allah ya ba su kyauta yadda ya ba mu, mu da muka gaskata da Ubangiji Yesu Kiristi, wane ni da zan yi hamayya da Allah?”
18 Men da de hørte dette, bleve de rolige, og de priste Gud og sagde: "Så har Gud også givet Hedningerne Omvendelsen til Liv."
Sa’ad da suka ji haka, ba su ƙara yin faɗa ba, suka kuma ɗaukaka Allah, suna cewa, “To, fa, har Al’ummai ma Allah ya sa suka tuba zuwa rai.”
19 De, som nu vare blevne adspredte på Grund af den Trængsel, som opstod i Anledning af Stefanus, vandrede om lige til Fønikien og Kypern og Antiokia, og de talte ikke Ordet til nogen uden til Jøder alene.
To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin da ya tashi a kan batun Istifanus suka tafi har Funisiya, Saifurus da kuma Antiyok, suna ba da saƙon ga Yahudawa kaɗai.
20 Men iblandt dem var der nogle Mænd fra Kypern og Kyrene, som kom til Antiokia og talte også til Grækerne og forkyndte Evangeliet om den Herre Jesus.
Amma waɗansunsu kuwa, mutane daga Saifurus da Sairin, suka je Antiyok suka fara yi wa Hellenawa magana su ma, suna ba da labari mai daɗi game da Ubangiji Yesu.
21 Og Herrens Hånd var med dem, og et stort Antal blev troende og omvendte sig til Herren.
Hannun Ubangiji kuwa yana tare da su, mutane da yawan gaske kuwa suka gaskata suka juya ga Ubangiji.
22 Men Rygtet om dem kom Menigheden i Jerusalem for Øre, og de sendte Barnabas ud til Antiokia.
Labari wannan abu ya kai kunnuwan ikkilisiya a Urushalima, sai suka aiki Barnabas zuwa Antiyok.
23 Da han nu kom derhen og så Guds Nåde, glædede han sig og formanede alle til med Hjertets Forsæt at blive ved Herren.
Da ya iso ya kuma ga tabbacin alherin Allah, sai ya yi farin ciki ya kuma ƙarfafa su duka su tsaya da gaskiya cikin Ubangiji da dukan zukatansu.
24 Thi han var en god Mand og fuld af den Helligånd og Tro. Og en, stor Skare blev ført til Herren.
Mutum ne nagari, cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, mutane masu yawan gaske kuwa suka juya ga Ubangiji.
25 Men han drog ud til Tarsus for at opsøge Saulus; og da han fandt ham, førte han ham til Antiokia.
Sa’an nan Barnabas ya tafi Tarshish don yă nemi Shawulu,
26 Og det skete, at de endog et helt År igennem færdedes sammen i Menigheden og lærte en stor Skare, og at Disciplene først i Antiokia bleve kaldte Kristne.
sa’ad da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antiyok. Ta haka shekara guda cur Barnabas da Shawulu suka yi suna taruwa da ikkilisiya, suka kuma koya wa mutane masu yawan gaske. A Antiyok ne aka fara kiran almajirai da suna Kirista.
27 Men i disse Dage kom der Profeter ned fra Jerusalem til Antiokia
A wannan lokaci waɗansu annabawa sun zo Antiyok daga Urushalima.
28 Og en af dem, ved Navn Agabus, stod op og tilkendegav ved Ånden, at der skulde komme en stor Hungersnød over hele Verden, hvilken også kom under Klaudius.
Ɗaya daga cikinsu mai suna Agabus, ya miƙe tsaye ya yi annabci ta wurin Ruhu cewa za a yi yunwa mai tsanani wadda za tă bazu a dukan duniyar Romawa (Wannan ya faru a zamanin mulkin Kalaudiyus.)
29 Men Disciplene besluttede at sende, hver efter sin Evne, noget til Hjælp for Brødrene, som boede i Judæa;
Kowanne a cikin almajiran, gwargwadon azancinsa, ya yanke shawara ya ba da gudummawa ga’yan’uwan da suke zama a Yahudiya.
30 hvilket de også gjorde, og de sendte det til de Ældste ved Barnabas og Saulus's Hånd.
Haka kuwa suka yi, suka aika da kyautarsa wa dattawan ikkilisiyar ta hannu Barnabas da Shawulu.

< Apostelenes gerninger 11 >