< Apostelenes gerninger 1 >
1 Den første Bog skrev jeg, o Theofilus! om alt det, som Jesus begyndte både at gøre og lære,
A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
2 indtil den Dag, da han blev optagen, efter at han havde givet Apostlene, som han havde udvalgt, Befaling ved den Helligånd;
har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
3 for hvem han også, efter at han havde lidt, fremstillede sig levende ved mange Beviser, idet han viste sig for dem i fyrretyve Dage og talte om de Ting, der høre til Guds Rige.
Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
4 Og medens han var sammen med dem, bød han dem, at de ikke måtte vige fra Jerusalem, men skulde oppebie Faderens Forjættelse, "hvorom," sagde han, "I have hørt af mig.
A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
5 Thi Johannes døbte med Vand; men I skulle døbes med den Helligånd om ikke mange Dage."
Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
6 Som de nu vare forsamlede, spurgte de ham og sagde: "Herre! opretter du på denne Tid Riget igen for Israel?"
Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
7 Men han sagde til dem: "Det tilkommer ikke eder at kende Tider eller Timer, hvilke Faderen har fastsat i sin egen Magt.
Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
8 Men I skulle få Kraft, når den Helligånd kommer over eder; og I skulle være mine Vidner både i Jerusalem og i hele Judæa og Samaria og indtil Jordens Ende."
Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
9 Og da han havde sagt dette, blev han optagen, medens de så derpå, og en Sky tog ham bort fra deres Øjne.
Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
10 Og som de stirrede op imod Himmelen, medens han for bort, se, da stode to Mænd hos dem i hvide Klæder,
Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
11 og de sagde: "I galilæiske Mænd, hvorfor stå I og se op imod Himmelen? Denne Jesus, som er optagen fra eder til Himmelen, skal komme igen på samme Måde, som I have set ham fare til Himmelen."
Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
12 Da vendte de tilbage til Jerusalem fra det Bjerg, som kaldes Oliebjerget og er nær ved Jerusalem, en Sabbatsvej derfra.
Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
13 Og da de kom derind, gik de op på den Sal, hvor de plejede at opholde sig, Peter og Johannes og Jakob og Andreas, Filip og Thomas, Bartholomæus og Matthæus, Jakob, Alfæus's Søn og Simon Zelotes, og Judas, Jakobs Søn.
Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
14 Alle disse vare endrægtigt vedholdende i Bønnen tillige med nogle Kvinder og Maria, Jesu Moder, og med hans Brødre.
Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
15 Og i disse Dage stod Peter op midt iblandt Brødrene og sagde: (og der var en Skare samlet på omtrent hundrede og tyve Personer):
A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
16 "I Mænd, Brødre! det Skriftens Ord burde opfyldes, som den Helligånd forud havde talt ved Davids Mund om Judas, der blev Vejleder for dem, som grebe Jesus;
ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
17 thi han var regnet iblandt os og havde fået denne Tjenestes Lod.
dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
18 Han erhvervede sig nu en Ager for sin Uretfærdigheds Løn, og han styrtede ned og brast itu, og alle hans Indvolde væltede ud,
(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
19 hvilket også er blevet vitterligt for alle dem, som bo i Jerusalem, så at den Ager kaldes på deres eget Mål Hakeldama, det er Blodager.
Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
20 Thi der er skrevet i Salmernes Bog: "Hans Bolig blive øde, og der være ingen, som bor i den," og: "Lad en anden få hans Tilsynsgerning."
Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
21 Derfor bør en af de Mænd, som vare sammen med os i hele den Tid, da den Herre Jesus gik ind og gik ud hos os,
Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
22 lige fra Johannes's Dåb indtil den Dag, da han blev optagen fra os, blive Vidne sammen med os om hans Opstandelse."
farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
23 Og de fremstillede to, Josef, som kaldtes Barsabbas med Tilnavn Justus, og Matthias.
Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
24 Og de bade og sagde: "Du Herre! som kender alles Hjerter, vis os den ene, som du har udvalgt af disse to
Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
25 til at få denne Tjenestes og Apostelgernings Plads, som Judas forlod for at gå hen til sit eget Sted."
ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
26 Og de kastede Lod imellem dem, og Loddet faldt på Matthias. og han blev regnet sammen med de elleve Apostle.
Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.