< 2 Samuel 8 >

1 Nogen Tid efter slog David Filisterne og undertvang dem, og David fratog Filisterne Meteg-Ha'amma.
Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
2 Fremdeles slog han Moabiterne, og han målte dem med en Snor, idet han lod dem lægge sig ned på Jorden og afmålte to Snorlængder, der skulde dræbes, og een, der skulde blive i Live. Således blev Moabiterne Davids skatskyldige Undersåtter.
Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
3 Ligeledes slog David Rehobs Søn, Kong Hadad'ezer af Zoba, da han var draget ud for at genoprette sit Herredømme ved Floden.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
4 David fratog ham 1700 Ryttere og 20000 Mand Fodfolk og lod alle Stridshestene lamme på hundrede nær, som han skånede.
Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
5 Og da Aramæerne fra Damaskus kom Hadad'ezer af Zoba til Hjælp, slog David 22000 Mand af Aramæerne.
Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
6 Derpå indsatte David Fogeder i det damaskenske Aram, og Aramæerne blev Davids skatskyldige Undersåtter. Således, gav HERREN David Sejr, overalt hvor han drog frem.
Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
7 Og David tog de Guldskjolde, Hadad'ezers Folk havde båret, og bragte dem til Jerusalem;
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
8 og fra Hadad'ezers Byer Teba og Berotaj bortførte Kong David Kobber i store Mængder.
Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
9 Men da Kong To'i af Hamat hørte, at David havde slået hele Hadad'ezers Stridsmagt,
Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
10 sendte han sin Søn Hadoram til Kong David for at hilse på ham og lykønske ham til, at han havde kæmpet med Hadad'ezer og slået ham - Hadad'ezer havde nemlig ligget i Krig med To'i - og han medbragte Sølv-, Guld- og Kobber-sager.
sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
11 Også dem helligede Kong David HERREN tillige med det Sølv og Guld, han havde helliget af Byttet fra alle de undertvungne Folk,
Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
12 Edom, Moab Ammoniterne, Filisterne, Amalek, og af det Bytte, han havde taget fra Rehobs Søn, Kong Hadad'ezer af Zoba.
wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
13 Og David vandt sig et Navn. Da han vendte tilbage fra Sejren over Aram, slog han Edom i Saltdalen, 18000 Mand;
Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
14 derpå indsatte han Fogeder i Edom; i hele Edom indsatte han Fogeder, og alle Edomiterne blev Davids Undersåtter, Således gav HERREN David Sejr, overalt hvor han drog frem.
Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
15 Og David var Konge over hele Israel, og han øvede Ret og Retfærdighed mod hele sit Folk.
Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
16 Joab, Zerujas Søn, var sat over Hæren; Josjafat, Ahiluds Søn, var Kansler;
Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
17 Zadok, Abitubs Søn, og Ebjatar, Ahimeleks Søn, var Præster; Seraja var Statsskriver;
Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
18 Benaja, Jojadas Søn, var sat over Kreterne og Pleterne, og Davids Sønner var Præster.
Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.

< 2 Samuel 8 >