< 2 Samuel 18 >

1 Derpå holdt David Mønstring over sit Mandskab og satte Tusindførere og Hundredførere over dem;
Dawuda ya tattara mutanen da suke tare da shi, ya naɗa musu komandodi na dubu-dubu, da na ɗari-ɗari.
2 og David delte Mandskabet i tre Dele; den ene Tredjedel stillede han under Joab, den anden under Abisjaj, Zerujas Søn og Joabs Broder, og den sidste Tredjedel under Gatiten Ittaj. Kongen sagde så til Folkene: "Jeg vil selv drage med i Kampen!"
Dawuda ya sa rundunoni kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Yowab, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Abishai, ɗan’uwan Yowab ɗan Zeruhiya, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Ittai mutumin Gat. Sai sarki ya ce wa rundunonin, “Tabbatacce zan tafi tare da ku.”
3 Men de svarede: "Du må ikke drage med; thi om vi flygter, ænser man ikke os; ja, selv om Halvdelen af os falder, ænser man ikke os, men du gælder lige så meget som ti Tusinde af os; derfor er det bedst, at du holder dig rede til at ile os til Hjælp fra Byen."
Amma mutanen suka ce, “Ba za ka fita ba; gama in ya kasance tilas mu gudu, ba za su kula da mu ba. Ko da rabinmu sun mutu, ba za su damu ba; amma kai kanka ka fi mutum dubu goma namu. Zai fi maka ka zauna a cikin gari, ka dinga aika mana da taimako.”
4 Kongen svarede: "Jeg gør, hvad I finder bedst!" Derpå stillede Kongen sig ved Porten, medens hele Mandskabet drog ud, hundredvis og tusindvis.
Sarki ya ce, “Zan yi duk abin da ya fi muku kyau.” Saboda haka sarki ya tsaya kusa da bakin ƙofa yayinda dukan mutane suke fitowa a ƙungiyar ɗari-ɗari da ta dubu-dubu.
5 Men Kongen gav Joab, Abisjajog Ittaj den Befaling: "Far nu lempeligt med den unge Absalon!" Og hele Mandskabet hørte, hvorledes Kongen gav alle Øversterne Befaling om Absalon.
Sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai, ya ce musu, “Ku yi mini hankali da saurayin nan Absalom.” Dukan mutane kuwa suka ji yadda sarki yake ba wa kowane komanda umarni.
6 Derpå rykkede Krigerne i Marken mod Israel, og Slaget kom til at stå i Efraims Skov.
Rundunonin suka tafi zuwa fili don su yi yaƙi da Isra’ila. Aka kuwa yi yaƙi a kurmin Efraim.
7 Der blev Israels Hær slået af Davids Folk, og der fandt et stort Mandefald Sted den Dag; der faldt 200000 Mand.
A nan ne mutanen Isra’ila suka sha kashi a hannun mutanen Dawuda. Waɗanda suka yi rauni da kuma waɗanda suka mutu a ranar sun yi yawa, mutum dubu ashirin.
8 Kampen bredte sig over hele Egnen, og Skoven fortærede den Dag flere Folk end Sværdet.
Yaƙin ya bazu a duk fāɗin ƙauyukan, abin da kurmin ya ci kawai a ranar ya fi yawan abin da aka kashe da takobi.
9 Absalon selv stødte på nogle af Davids Folk; Absalon red på sit Muldyr, og da Muldyret kom ind under en stor Terebintes tætte Grene, blev hans Hoved hængende i Terebinten, så han hang mellem Himmel og Jord, medens Muldyret, han sad på, løb bort.
To, Absalom ya haɗu da mutanen Dawuda. Yana hawan dokinsa, kuma yayinda dokin ya kusa kai cikin rassan babban itacen oak, sai kan Absalom ya sarƙafe a kan itacen oak ɗin. Dokin ya wuce da gudu, shi kuwa ya rataye a can yana lilo.
10 En Mand, der så det meldte det til Joab og sagde: "Jeg så Absalon hænge i en Terebinte."
Sa’ad da wani daga cikin mutanen ya gan haka, sai ya gaya wa Yowab, “Na ga Absalom yana rataye a itacen oak.”
11 Da sagde Joab til Manden, der havde meldt ham det: "Når du så det, hvorfor slog du ham da ikke til Jorden med det samme? Så havde jeg givet dig ti Sekel Sølv og et Bælte!"
Yowab ya ce wa mutumin da ya ba shi labarin, “Mene! Ka ga shi? Don me ba ka buge shi har ƙasa nan da nan ba? Ai, da na ba ka shekel goma na azurfa da abin ɗamarar jarumi.”
12 Men Manden svarede Joab: "Om jeg så havde fået tilvejet tusind Sekel, havde jeg ikke lagt Hånd på Kongens Søn; thi vi hørte jo selv, hvorledes Kongen bød dig, Abisjaj og Ittaj: Vogt vel på den unge Absalon!
Amma mutumin ya ce wa Yowab, “Ko da za a auna mini azurfa dubu a hannuna, ba zan miƙa hannuna in taɓa ɗan sarki ba. A kunnuwanmu fa sarki ya umarce ka, da Abishai, da Ittai cewa, ‘Ku tsare saurayin nan Absalom a madadina.’
13 Dersom jeg havde handlet svigefuldt imod ham -intet bliver jo skjult for Kongen - vilde du have ladet mig i Stikken!"
Da na yi haka da na sa kaina a halin ƙaƙa-ni-ka-yi, kuma babu abin da zai ɓoyu ga sarki, kai kuwa za ka janye abinka daga gare ni.”
14 Da sagde Joab: "Så gør jeg det for dig!" Dermed greb han tre Spyd og stødte dem i Brystet på Absalon, som endnu levede og hang mellem Terebintens Grene.
Yowab ya ce, “Ba zan ɓata lokaci da kai ba.” Saboda haka sai ya ɗauki māsu uku a hannunsa ya zura su a ƙahon zuciyar Absalom, tun Absalom yana da sauran rai a maƙale a itacen oak.
15 Derpå trådte ti unge Mænd, der var Joabs Våbendragere, til og gav Absalon Dødsstødet.
Masu ɗaukan kayan yaƙin Yowab goma kuwa sun kewaye Absalom, suka bubbuge shi suka kashe.
16 Joab lod nu støde i Hornet, og Hæren opgav at forfølge Israel, thi Joab bød Folkene standse.
Sa’an nan Yowab ya busa ƙaho, sai sojoji suka bar fafaran Isra’ila, gama Yowab ya tsai da su.
17 Derpå tog de og kastede Absalon i en stor Grube i Skoven og ophobede en mægtig Stendynge over ham. Og hele Israel flygtede hver til sit.
Suka ɗauki Absalom, suka jefa shi cikin wani babban rami a kurmin, suka kuwa tula tsibin duwatsu a kansa. Ana cikin haka, sai dukan Isra’ilawa suka tsere zuwa gidajensu.
18 Men medens Absalon endnu levede, havde han taget og rejst sig den Stenstøtte, som står i Kongedalen; thi han sagde: "Jeg har ingen Søn til at bevare Mindet om mit Navn." Han havde opkaldt Stenstøtten efter sig selv, og endnu den Dag i Dag kaldes den "Absalons Minde".
A lokacin da Absalom yake da rai, Absalom ya gina wa kansa al’amudin tunawa, a Kwarin Sarki, gama ya yi tunani ya ce, “Ba ni da ɗa namiji wanda zai sa a riƙa tunawa da ni.” Sai ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kuwa kira shi Al’amudin Absalom har wa yau.
19 Da sagde Ahima'az, Zadoks Søn: "Lad mig løbe hen og bringe Kongen den gode Tidende, at HERREN har skaffet ham Ret over for hans Fjender!"
Ahimawaz ɗan Zadok ya ce, “Bari in ruga in kai wa sarki labari cewa Ubangiji ya cece shi daga hannun abokan gābansa.”
20 Men Joab svarede ham: "Du skal ikke være den, der bringer Bud i Dag; en anden Gang kan du bringe Bud, men i bag skal du ikke gøre det, da Kongens Søn er død!"
Yowab ya ce, “Ba kai ba ne za ka kai wannan labari a yau ba. Kana iya kai labarin wani lokaci, amma yau kam ba zai yiwu ba, saboda ɗan sarki ya mutu.”
21 Og Joab sagde til Etiopieren: "Gå du hen og meld Kongen, hvad du har set!" Da kastede Etiopieren sig til Jorden for Joab og ilede af Sted.
Sai Yowab ya ce wa wani mutumin Kush, “Je ka faɗa wa sarki abin da ka gani.” Mutumin Kush ɗin kuwa ya rusuna wa Yowab, sai ya ruga a guje.
22 Men Ahima'az, Zadoks Søn, sagde atter til Joab: "Ske, hvad der vil! Lad også mig løbe bag efter Etiopieren!" Da sagde Joab: "Hvorfor vil du det, min Søn? For dig er der ingen Budløn at hente!"
Ahimawaz ɗan Zadok ya sāke ce wa Yowab, “Ko mene ne zai faru, ina roƙonka bari in bi bayan mutumin Kush nan.” Amma Yowab ya ce, “Ɗana me ya sa kake so ka je? Ba ka da labarin da zai jawo maka lada.”
23 Men han blev ved: "Ske, hvad der vil! Jeg løber!" Så sagde han: "Løb da!" Og Ahima'az løb ad Vejen gennem Jordanegnen og nåede frem før Etiopieren.
Ya ce, “Ko mene ne zai faru, ina so in ruga da gudu.” Sai Yowab ya ce, “Ruga!” Sai Ahimawaz ya sheƙa a guje ya bi ta hanyar fili ya riga mutumin Kush nan.
24 David sad just mellem de to Porte, og Vægteren steg op på Porttaget ved Muren; da han så ud, se, da kom en Mand løbende alene.
Yayinda Dawuda yake zaune tsakanin ƙofofin ciki da na waje, sai mai tsaro ya hau rufin ginin da yake kan hanyar shiga ta wajen katanga. Da ya duba sai ya ga wani mutum shi kaɗai yana gudu.
25 Vægteren råbte og meldte det til Kongen, og Kongen sagde: "Er han alene, har han Bud at bringe!" Men medens Manden fortsatte sit Løb og kom nærmere,
Mai tsaro ya tā da murya ya faɗa wa sarki. Sarki ya ce, “In shi kaɗai ne, ya kawo labari mai kyau ke nan.” Mutumin ya matso kusa-kusa.
26 så Vægteren en anden Mand komme løbende og råbte ned i Porten: "Der kommer een Mand til løbende alene!" Kongen sagde: "Også han har Bud at bringe!"
Sai mai tsaron ya ga wani mutum yana zuwa a guje. Sai ya tā da murya ya kira mai tsaron ƙofa ya ce, “Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai!” Sarki ya ce, “Shi ma yana kawo labari mai daɗi ne.”
27 Da råbte Vægteren: "Den forreste løber således, at det ser ud til at være Ahima'az, Zadoks Søn!" Kongen sagde: "Det er en god Mand, han kommer med godt Bud!"
Sai mai tsaron ya ce, “A ganina gudu na farin, ya yi kama da gudun Ahimawaz, ɗan Zadok.” Sarki ya ce, “Shi mutumin kirki ne, yana zuwa da saƙo mai kyau.”
28 Imidlertid var Ahima'az kommet nærmere og råbte til Kongen: "Hil dig!" Så kastede han sig ned på Jorden for Kongen og sagde: "Lovet være HERREN din Gud, som gav dem, der løftede Hånd mod min Herre Kongen, i din Hånd!"
Sai Ahimawaz ya tā da murya ya ce wa sarki, “Kome lafiya yake!” Sai ya rusuna har ƙasa a gaban sarki ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka! Ya ba da mutanen da suka tayar wa ranka yă daɗe a hannunsa.”
29 Kongen spurgte: "Er den unge Absalon uskadt?" Ahima'az svarede: "Jeg så, at der var stor Tummel, da Kongens Træl Joab sendte din Træl af Sted, men jeg ved ikke, hvad det var."
Sai sarki ya ce, “Saurayin nan Absalom yana nan da rai?” Ahimawaz ya ce, “Na ga wani babban rikicewar a daidai lokacin da Yowab yake gab da aikan bawan sarki da kuma ni, sai dai ban san ko mene ne ba.”
30 Kongen sagde da: "Træd til Side og stil dig der!" Og han trådte til Side og blev stående.
Sai sarki ya ce, “Koma gefe ka jira a can.” Sai ya ja gefe ya tsaya.
31 I det samme kom Etiopieren; og Etiopieren sagde: "Der er Bud til min Herre Kongen: HERREN har i Dag skaffet dig Ret over for alle dine Modstandere!"
Sai ga mutumin Kush ya iso ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, ka ji labari mai kyau! Ubangiji ya cece ka yau daga dukan waɗanda suka tayar maka.”
32 Kongen spurgte Etiopieren: "Er den unge Absalon uskadt?" Og han svarede: "Det gå min Herre Kongens Fjender og alle dine Modstandere som den unge Mand!"
Sarki ya ce wa mutumin Kush, “Saurayin nan Absalom, yana nan lafiya?” Mutumin Kush ya ce, “Allah yă sa abokan gāban ranka yă daɗe, da duk waɗanda suka tayar maka da mugunta, su zama kamar saurayin nan.”
33 Da blev Kongen dybt rystet, og han gik op i Stuen på Taget over Porten og græd; og han gik frem og tilbage og klagede: Min Søn Absalon, min Søn, min Søn Absalon! Var jeg blot død i dit Sted! Absalon, min Søn, min Søn!"
Sai gaban sarki ya faɗi. Ya haura zuwa ɗakin da yake kan katangar hanyar shiga ya yi kuka. Yayinda yake tafiya ya ce, “Ya ɗana Absalom! Ɗana, ɗana Absalom! Da ma a ce ni ne na mutu maimakonka. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”

< 2 Samuel 18 >