< 2 Samuel 13 >

1 Nogen Tid efter tildrog følgende sig. Davids Søn Absalon havde en smuk Søster, som hed Tamar, og Davids Søn Amnon fattede Kærlighed til hende.
Ana nan sai Amnon ɗan Dawuda ya fara son Tamar, kyakkyawar’yar’uwar Absalom ɗan Dawuda.
2 Amnon blev syg af Attrå efter sin Søster Tamar; thi hun var Jomfru, og Amnon øjnede ingen Mulighed for at få sin Vilje med hende.
Amnon ya matsu ƙwarai har abin ya sa shi ciwo saboda ƙanuwarsa Tamar. Ya gane zai zama da wuya yă sadu da Tamar ita kaɗai, gama ba ta taɓa kwana da namiji ba.
3 Men Amnon havde en Ven ved Navn Jonadab, en Søn af Davids Broder Sjim'a, og denne Jonadab var en såre klog Mand;
To, Amnon yana da wani aboki mai suna Yonadab, ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda. Yonadab dai mai wayo ne ƙwarai.
4 han sagde til ham: "Hvorfor er du så elendig hver Morgen, Kongesøn? Vil du ikke sige mig det?" Amnon svarede: "Jeg elsker min Broder Absalons Søster Tamar!"
Ya tambayi Amnon ya ce, “Don me kowace safiya fuskarka a ɓace take? Kai ba yaron sarki ba ne? Faɗa mini, me ke faruwa?” Amnon ya ce masa, “Ina son Tamar ƙanuwar wan nawa Absalom ne.”
5 Da sagde Jonadab til ham: "Læg dig til Sengs og lad, som du er syg! Når så din Fader kommer for at se til dig, skal du sige: Lad min Søster Tamar komme og give mig noget at spise! Når hun laver Maden i mit Påsyn, så at jeg kan se det, og hun selv giver mig den, kan jeg spise."
Yonadab ya ce, “Je gado ka kwanta kamar ba ka da lafiya. Sa’ad da mahaifinka ya zo ganinka, sai ka ce masa, ‘Ina so ƙanuwata Tamar tă kawo mini wani abu in ci. Bari tă shirya abincin a gabana don in ganta, in kuma ci daga hannunta.’”
6 Så gik Amnon til Sengs og lod. som han var syg; og da Kongen kom for at se til ham, sagde Amnon til Kongen: "Lad min Søster Tamar komme og lave et Par Kager i mit Påsyn og selv give mig dem: så kan jeg spise."
Sai Amnon ya kwanta sai ka ce yana ciwo. Da sarki ya zo don ganinsa, sai Amnon ya ce, “Zan so ƙanuwata Tamar tă zo tă shirya mini abinci a gabana, don in ci daga hannunta.”
7 David sendte da Bud ind i Huset til Tamar og lod sige: "Gå over til din Broder Amnons Hus og lav Mad til ham!"
Dawuda kuwa ya aika wa Tamar a fada, ya ce, “Ki je gidan Amnon ɗan’uwanki, ki yi masa abinci.”
8 Og Tamar gik over til sin Broder Amnons Hus, hvor han lå til Sengs, tog Dejen, æltede den og lavede Kagerne i hans Påsyn og bagte dem;
Saboda haka Tamar ta tafi gidan ɗan’uwanta Amnon, wanda yake kwance. Ta ɗauki fulawa, ta kwaɓa, ta yi burodi a gabansa ta toya shi.
9 derpå tog hun Panden og hældte dem ud i hans Påsyn; Amnon vilde dog ikke spise, men sagde: "Lad alle gå udenfor!" Og da de alle var gået udenfor,
Sa’an nan ta juye a kasko ta ba shi burodin, amma ya ƙi ci. Amnon ya ce, “A sa kowa yă fita daga nan.” Saboda haka kowa ya fita ya bar shi.
10 sagde Amnon til Tamar: "Bær Maden ind i Inderværelset og lad mig få den af din egen Hånd!" Da tog Tamar Kagerne, som hun havde lavet, og bar dem ind i Inderværelset til sin Broder Amnon.
Sa’an nan Amnon ya ce wa Tamar, “Kawo abincin a nan a cikin ɗakin kwanciyata, don in ci daga hannunki.” Tamar kuwa ta ɗauki burodin da ta toya, ta kawo wa ɗan’uwanta Amnon a ciki ɗakin kwanciyarsa.
11 Men da hun bar dem hen til ham, for at han skulde spise, greb han fat i hende og sagde: "Kom og lig hos mig, Søster!"
Amma da ta kai masa don yă ci, sai ya cafke ta ya ce, “Zo in kwana da ke,’yar’uwata.”
12 Men hun sagde: "Nej, Broder! Krænk mig ikke! Således gør man ikke i Israel! Øv dog ikke denne Skændselsdåd!
Ta ce, “Kada ka yi wannan ɗan’uwana! Kada ka tilasta ni. Bai kamata a yi irin wannan abu a Isra’ila ba! Kada ka yi wannan mugun abu.
13 Hvor skulde jeg gå hen med min Skam? Og du vilde blive regnet blandt Dårer i Israel! Tal hellere med Kongen; han nægter dig ikke at få mig!"
Ni fa, ina zan sa kaina saboda kunya? Kai kuma za ka zama kamar wani mugun wawa a Isra’ila. Ina roƙonka ka yi wa sarki magana; ba zai hana ni aurenka ba.”
14 Han, vilde dog ikke høre hende, men tog hende med Vold, krænkede hende og lå hos hende.
Amma Amnon ya ƙi yă saurare ta, da yake ya fi ta ƙarfi, sai ya yi mata fyaɗe.
15 Men bagefter hadede Amnon hende med et såre stort Had; ja det Had, han følte mod hende, var større end den Kærlighed, han havde båret til hende. Og Amnon sagde til hende: "Stå op og gå din Vej!"
Bayan ya yi lalata da ita sai Amnon ya ƙi ta da mummunan ƙiyayya. Zahiri ya ƙi ta fiye da ya ƙaunace ta. Sai Amnon ya ce mata, “Tashi, ki fita!”
16 Da sagde hun til ham: "Nej, Broder! Den Udåd, at du nu jager mig bort, er endnu større end den anden, du øvede imod mig!" Han vilde dog ikke høre hende,
Ta ce, “A’a! Korina zai fi muni da abin da ka riga ka yi mini.” Amma ya ƙi yă saurare ta.
17 men kaldte på den unge Mand, der var hans Tjener, og sagde: "Få mig hende der ud af Huset og stæng Døren efter hende!"
Sai ya kira bawansa ya ce, “Fitar da matan nan daga nan, ka rufe ƙofa.”
18 Hun bar en fodsid Kjortel med Ærmer; thi således klædte Jomfruerne blandt Kongedøtrene sig fordum. Tjeneren førte hende da ud af Huset og stængede Døren efter hende.
Saboda haka bawansa ya fitar da ita, ya kuma sa aka rufe ƙofa. Tana sanye da doguwar riga mai kayan ado masu tsada, gama wannan ne irin kayan da budurwai’ya’yan sarki mata suke sawa.
19 Men Tamar strøede Aske på sit Hoved og sønderrev den fodside Kjortel, hun havde på, og tog sig til Hovedet og skreg ustandseligt, medens hun gik bort.
Sai Tamar ta zuba toka a kanta, ta kuma yayyage doguwar riga mai kayan adon da take sanye da shi. Ta sa hannunta a kai, ta tafi tana kuka da ƙarfi.
20 Da sagde hendes Broder Absalon til hende: "Har din Broder Amnon været hos dig? Ti nu stille, Søster! Han er jo din Broder; tag dig ikke den Sag nær!" Tamar sad da ensom hen i sin Broder Absalons Hus.
Absalom ɗan’uwanta ya ce mata, “Amnon, ɗan’uwanki ya ɓata ki ko? To, ki yi shiru’yar’uwata; ai, ɗan’uwanki ne. Kada wannan abu yă dame ki.” Tamar kuwa ta zauna a gidan ɗan’uwanta Absalom, zaman kaɗaici.
21 Da Kong David hørte alt dette, blev han meget vred; men han bebrejdede ikke sin Søn Amnon noget, thi han elskede ham, fordi han var hans førstefødte.
Da Sarki Dawuda ya ji dukan abin da ya faru, sai ya husata ƙwarai.
22 Og Absalon talte ikke til Amnon, hverken ondt eller godt; thi Absalon hadede Amnon, fordi han havde krænket hans Søster Tamar.
Absalom kuwa bai yi wa Amnon wata magana ta alheri ko ta mugunta ba; ya ƙi jinin Amnon domin ya ci mutuncin ƙanuwarsa Tamar.
23 Men et Par År efter holdt Absalon Fåreklipning i Ba'al-Hazor, som ligger ved Efraim, og dertil indbød Absalon alle Kongesønnerne.
Bayan shekaru biyu, sa’ad da masu askin tumakin Absalom suna Ba’al-Hazor, kusa da iyakar Efraim, sai ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza a can.
24 Absalon kom til Kongen og sagde: "Se, din Træl holder Fåreklipning; vil ikke Kongen og hans Folk tage med din Træl derhen?"
Sai Absalom ya je wurin sarki ya ce, “Bawanka ya sa masu askin tumaki sun zo. Ko sarki da fadawansa za su zo tare da ni?”
25 Men Kongen sagde til Absalon: "Nej, min Søn! Vi vil ikke alle gå med, for at vi ikke skal falde dig til Byrde!" Og skønt han nødte ham, vilde han ikke gå med, men tog Afsked med ham.
Sarki ya ce, “A’a ɗana, bai kamata dukanmu mu tafi ba; don kada nauyi yă yi maka yawa.” Absalom dai ya dāge, duk da haka sarki ya ƙi yă je, sai dai ya albarkace shi.
26 Da sagde Absalon: "Så lad i alt Fald min Broder Amnon gå med!" Men Kongen sagde til ham: "Hvorfor skal han med?"
Sa’an nan Absalom ya ce, to, “In ba za ka ba, ina roƙonka bari Amnon ɗan’uwana yă zo tare da mu.” Sarki ya ce masa, “Don me zai tafi tare da kai?”
27 Da Absalon nødte ham, lod han dog Amnon og de andre Kongesønner gå med. Og Absalon gjorde et kongeligt Gæstebud.
Amma Absalom ya nace don sarki yă yarda, saboda haka sarki ya bar Amnon da sauran’ya’yan sarki maza su tafi tare da shi.
28 Men Absalon gav sine Folk den Befaling: "Pas på, når Vinen er gået Amnon til Hovedet; når jeg så siger til eder: Hug Amnon ned! dræb ham så! Frygt ikke; det er mig, som befaler jer det. Tag Mod til jer og vis jer som kække Mænd!"
Absalom ya umarci mutanensa ya ce, “Ku saurara! Sa’ad da Amnon ya bugu sosai da giya na kuma ce muku, ‘Ku bugi Amnon,’ sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro. Ashe, ba ni ne na ba ku wannan umarni ba? Ku yi ƙarfin hali, ku kuma yi jaruntaka.”
29 Absalons Folk gjorde ved Amnon, som Absalon havde befalet. Da brød alle Kongesønnerne op, besteg deres Muldyr og flyede.
Saboda haka mutanen Absalom suka yi wa Amnon abin da Absalom ya umarta. Sai dukan sauran’ya’yan sarki maza suka hau dawakansu suka gudu.
30 Medens de endnu var undervejs, nåede det Rygte David: "Absalon har hugget alle Kongesønnerne ned, ikke en eneste er tilbage af dem!"
Yayinda suke kan hanyarsu, sai labari ya kai kunnen Dawuda cewa, “Absalom ya kashe dukan’ya’yan sarki maza; ko ɗayansu Absalom bai rage ba.”
31 Da stod Kongen op, sønderrev sine Klæder og lagde sig på Jorden; også alle hans Folk, som stod hos, sønderrev deres Klæder.
Sai sarki ya tashi, ya yage tufafinsa, ya kuma kwanta a ƙasa; dukan bayinsa kuwa suka tsaya da rigunansu yagaggu.
32 Men Jonadab Davids Broder Sjim'as Søn, tog til Orde og sagde: "Min Herre må ikke tro, at de har dræbt alle de unge Kongesønner; kun Amnon er død, thi der har været noget ved Absalons Mund, som ikke varslede godt, lige siden den Dag Amnon krænkede hans Søster Tamar.
Amma Yonadab, ɗan Shimeya ɗan’uwan Dawuda ya ce, “Kada ranka yă daɗe yă yi tunani cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza; Amnon ne kaɗai ya mutu. Wannan ce niyyar Absalom tun lokacin da Amnon ya yi wa Tamar’yar’uwansa fyaɗe.
33 Derfor må min Herre Kongen ikke, tage sig det nær og tro, at alle Kongesønnerne er døde. Kun Amnon er død!"
Kada mai girma sarki yă damu da jita-jitan nan cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza. Amnon ne kaɗai ya mutu.”
34 Da den unge Mand, som holdt Udkig, så ud, fik han Øje på en Mængde Mennesker, som kom ned ad Skråningen på Vejen til Horonajim, og han gik ind og meldte Kongen: "Jeg kan se, der kommer Mennesker ned ad Bjergsiden på Vejen til Horonajim."
Ana cikin haka, sai Absalom ya gudu. To, mutumin da yake tsaro a wannan lokaci ya ɗaga kai sai ya ga mutane da yawa a hanya, yamma da shi, suna gangarowa daga gefen tudu. Sai mai tsaron ya je ya gaya wa sarki cewa, “Na ga mutane ta wajen Horonayim, a gefen tudu.”
35 Da sagde Jonadab til Kongen: "Der kommer Kongesønnerne; det er, som din Træl sagde!"
Yonadab ya ce wa Sarki, “Duba, ga’ya’yan sarki maza sun zo; ya faru kamar dai yadda bawanka ya faɗa.”
36 Og som han havde sagt det, kom Kongesønnerne, og de brast i Gråd; også Kongen og alle hans folk brast i heftig Gråd.
Yana gama magana, sai ga’ya’yan sarki maza suka shigo suna kuka da ƙarfi. Sarki ma da dukan bayinsa suka yi kuka mai zafi.
37 Men Absalon flygtede og begav sig til Kong Talmaj, Ammihuds Søn, i Gesjur. Og Kongen sørgede over sin Søn i al den Tid.
Absalom ya gudu ya tafi wurin Talmai ɗan Ammihud, sarkin Geshur. Amma Sarki Dawuda ya yi ta makokin ɗansa kowace rana.
38 Da Absalon flygtede, begav han sig til Gesjur, og der blev han tre År.
Bayan Absalom ya gudu sai ya je wurin Geshur, ya zauna a can shekara uku.
39 Men Kongen begyndte at længes inderligt efter Absalon, thi han havde trøstet sig over Amnons Død.
Sai zuciyar sarki Dawuda ya komo kan Absalom, gama an yi masa ta’aziyya game da mutuwar Amnon.

< 2 Samuel 13 >