< Anden Kongebog 24 >

1 I hans Dage drog Kong Nebukadnezar af Balel op, og Jojakim underkastede sig ham; men efter tre Års Forløb faldt han fra ham igen.
A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
2 Da sendte HERREN kaldæiske, aramaiske, moabitiske og ammonitiske Strejfskarer imod ham; dem sendte han ind i Juda for at ødelægge det efter det Ord, HERREN havde talet ved sine Tjenere Profeterne.
Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
3 Det skyldtes ene og alene HERRENs Vrede, at Juda blev drevet bort fra HERRENs Åsyn; det var for Manasses Synders Skyld, for alt det, han havde gjort,
Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
4 også for det uskyldige Blods Skyld, som han havde udgydt så meget af, at han havde fyldt Jerusalem dermed; det vilde HERREN ikke tilgive.
haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
5 Hvad der ellers er at fortælle om Jojakim, alt, hvad han udførte, står jo optegnet i Judas Kongers Krønike.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
6 Så lagde Jojakim sig til Hvile hos sine Fædre; og hans Søn Jojakin blev Kooge i hans Sted.
Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
7 Men Ægypterkongen drog ikke mere ud af sit Land, thi Babels Konge havde taget alt, hvad der tilhørte Ægypterkongen fra Ægyptens Bæk til Eufratfloden.
Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
8 Jojakin var atten År gammel, da han blev Konge, og han herskede tre Måneder i Jerusålem. Hans Moder hed Nehusjta og var en Datter af Elnatan fra Jerusalem.
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
9 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENs Øjne, ganske som hans Fader.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
10 På den Tid drog Kong Nebukadnezar af Babels Folk op mod Jerusalem, og Byen blev belejret.
A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
11 Kong Nebukadnezar af Babel kom til Jerusalem, medens hans Folk belejrede det.
Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
12 Da overgav Kong Jojakin af Juda sig med sin Modet, sine Tjenere, Øverster og Hoffolk til Babels Konge, og han tog imod ham; det var i Kongen af Babels ottende Regeringsår.
Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
13 Og som HERREN havde forudsagt, førte han alle Skattene i HERRENs Hus og Kongens Palads bort og brød Guldet af alle de Ting, Kong Salomo af Israel havde ladet lave i HERRENs Helligdom.
Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
14 Og han førte hele Jerusalem, alle Øversterne og de velhavende, 10.000 i Tal, bort som Fanger, ligeledes Grovsmede og Låsesmede, så der ikke blev andre tilbage end de fattigste af Folket fra Landet.
Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
15 Så førte han Jojakin som Fange til Babel, også Kongens Moder og Hustruer, hans Hoffolk og alle de højtstående i Landet førte han som Fanger fra Jerusalem til Babel;
Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
16 fremdeles alle de velbavende, 7000 i Tal, Grovsmedene og Låsesmedene, 1800 i Tal, alle øvede Krigere - dem førte Babels Konge som Fanger til Babel.
Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
17 Men i Jojakins Sted gjorde Babels Konge hans Farbroder Mattanja til Konge, og han ændrede hans Navn til Zedekias.
Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
18 Zedekias var een og tyve År gammel, da han blev Konge, og han herskede elleve År i Jerusalem. Hans Moder hed Hamital og var en Datter af Jirmeja fra Libna.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
19 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENs Øjne, ganske som Jojakim.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
20 Thi for HERRENs Vredes Skyld timedes dette Jerusalem og Juda, og til sidst stødte han dem bort fra sit Åsyn. Og Zedekias faldt fra Babels Konge.
Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.

< Anden Kongebog 24 >