< Anden Kongebog 2 >
1 Dengang HERREN ville lade Elias fare op til Himmelen i et Stormvejr, gik Elias fra Gilgal.
Da lokaci ya yi da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa sama cikin guguwa, Iliya da Elisha kuwa suna kan hanyarsu daga Gilgal.
2 Og Elias sagde til Elisa: "Bliv her, thi HERREN vil have mig til Betel!" Men Elisa svarede: "Så sandt HERREN lever, og så sandt du lever, jeg går ikke fra dig!" De gik da ned til Betel.
Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka dakata a nan; Ubangiji ya aike ni Betel.” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka gangara zuwa Betel.
3 Så kom Profetsønnerne i Betel ud til Elisa og sagde til ham: "Ved du, at HERREN i dag vil tage din Herre bort fra dig?" Han svarede: "Ja, jeg ved det, ti kun stille!"
Sai ƙungiyar annabawa a Betel suka fito zuwa wajen Elisha suka ce masa, “Ka san cewa Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga wurinka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma kada ku yi magana game da wannan.”
4 Derpå sagde Elias til ham: "Bliv her, Elisa, thi HERREN vil have mig til Jeriko!" Men han svarede: "Så sandt HERREN lever, og så sandt du lever, jeg går ikke fra dig!" De kom da til Jeriko.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan Elisha; Ubangiji ya aike ni Yeriko.” Sai ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai ma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka sai suka tafi Yeriko.
5 Men Profetsønnerne i Jeriko trådte hen til Elisa og sagde til ham: "Ved du, at HERREN i Dag vil tage din Herre bort fra dig?" Han svarede: "Ja, jeg ved det, ti kun stille!"
Ƙungiyar annabawa a Yeriko suka haura zuwa wajen Elisha suka ce, “Ko ka san Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga gare ka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma ku bar zancen nan tukuna.”
6 Derpå sagde Elias til ham: "Bliv her, thi HERREN vil have mig til Jordan!" Men han svarede: "Så sandt HERREN lever, og så sandt du lever, jeg går ikke fra dig!" Så fulgtes de ad.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan, Ubangiji ya aike ni Urdun.” Sai Elisha ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka ci gaba da tafiya tare.
7 Men halvtredsindstyve af Profetsønnerne gik hen og stillede sig et godt Stykke derfra, medens de to stod ved Jordan.
Mutum hamsin na ƙungiyar annabawa suka je suka tsaya da nisa, suna fuskantar inda Iliya da Elisha suka tsaya a Urdun.
8 Elias tog nu sin Kappe, rullede den sammen og slog Vandet med den; da skiltes det ad, og de gik begge over på tør Bund.
Sai Iliya ya tuɓe rigarsa, ya nannaɗe ya bugi ruwan Urdun da shi. Sai ruwan ya dāre gida biyu, suka haye a busasshiyar ƙasa.
9 Og da de var kommet over, sagde Elias til Elisa: "Sig, hvad du ønsker, jeg skal gøre for dig, før jeg tages bort fra dig!" Elisa svarede: "Måtte to Dele af din Ånd komme over mig!"
Da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Faɗi mini, abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka!” Elisha ya amsa ya ce, “Bari in gāji ninki biyu na ruhunka.”
10 Da sagde han: "Det er et stort Forlangende, du kommer med! Dersom du ser mig, når jeg tages bort fra dig, skal det blive dig til Del, ellers ikke!"
Iliya ya ce, “Ka nemi abu mai wuya, amma in ka ga lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, zai zama naka, in ba haka ba, ba za ka samu ba ke nan.”
11 Medens de nu gik og talte sammen, se, da kom en lldvogn og Ildheste og skilte dem ad, og Elias for op til Himmelen i Stormvejret.
Yayinda suke tafiya suna magana, sai kwatsam, keken yaƙin wuta da dawakan wuta suka ratse tsakaninsu, sai Iliya ya tafi sama a cikin guguwa.
12 Og Elisa så det og råbte: "Min Fader, min Fader, du Israels Vogne og Ryttere!" Og han så ham ikke mere. Så greb han sine Klæder og sønderrev dem.
Da Elisha ya ga haka sai ya yi ihu yana cewa, “Babana! Babana! Kekunan yaƙin da mahayan dawakan Isra’ila!” Elisha kuwa bai sāke ganinsa ba. Sai ya kama tufafinsa ya yayyage.
13 Derpå tog han Elias's Kappe, som var faldet af ham, op og gik tilbage og stillede sig ved Jordans Bred,
Sai ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya koma ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun.
14 og han tog Elias's Kappe, som var faldet af ham, slog Vandet med den og sagde: "Hvor er nu HERREN, Elias's Gud?" Og da han havde slået Vandet, skiltes det ad, og Elisa gik over.
Sa’an nan Elisha ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya bugi ruwan da shi. Ya ce, “Yanzu ina Ubangiji Allah na Iliya?” Da ya bugi ruwan sai ruwan ya dāre gida biyu, sai ya haye.
15 Da Profetsønnerne fra Jeriko så det derovre, sagde de: "Elias's Ånd hviler på Elisa!" Og de gik ham i Møde og kastede sig til Jorden for ham.
Ƙungiyar annabawa daga Yeriko, waɗanda suke kallo, suka ce, “Ruhun Iliya yana a kan Elisha.” Sai suka je su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa.
16 Derpå sagde de til ham: "Se, her hos dine Trælle er der halvtredsindstyve raske Mænd, lad dem gå ud og lede efter din Herre; måske HERRENs Ånd har taget ham og kastet ham hen på et af Bjergene eller i en af Dalene!" Men han svarede: "I skal ikke sende dem af Sted!"
Suka ce, “Duba, mu bayinka muna da masu ji da ƙarfi hamsin. Bari su je su nemi maigidanka. Wataƙila, Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi ya ajiye bisa wani dutse, ko wani kwari.” Elisha ya ce, “A’a, kada ku aike su.”
17 Men da de blev ved at trænge ind på ham, sagde han: "Så send dem da af Sted!" Så sendte de halvtredsindstyve Mænd ud, og de ledte efter ham i tre Dage, men fandt ham ikke.
Amma suka matsa masa har ya ji ba ya iya hana su. Saboda haka ya ce, “Ku aike su.” Sai suka aiki mutane hamsin, suka yi ta nema har kwana uku amma ba su same Iliya ba.
18 Og da de kom tilbage, medens han endnu var i Jeriko, sagde han til dem: "Sagde jeg ikke til eder, at I ikke skulde gå?"
Da suka dawo wurin Elisha, wanda yake a Yeriko, sai ya ce musu, “Ban ce muku kada ku tafi ba?”
19 Mændene i Byen sagde til Elisa: "Byen ligger godt nok, som min Herre ser, men Vandet er dårligt og volder utidige Fødsler i Egnen."
Mutane garin suka ce wa Elisha, “Ranka yă daɗe, duba, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba shi da kyau, ƙasar kuma ba ta ba da amfani.”
20 Da sagde han: "Hent mig en ny Skål og kom Salt deri!" Og de hentede den til ham.
Sai ya ce, “Ku kawo mini sabuwar ƙwarya, ku kuma sa gishiri a ciki.” Sai suka kawo masa.
21 Så gik han ned til Kildevældet og kastede Salt deri, idet han sagde: "Så siger HERREN: Jeg gør dette Vand sundt, så at der ikke mer skal komme Død eller utidige Fødsler deraf!"
Sai ya tafi maɓulɓular ruwan yana watsa gishirin a ciki, yana cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da ruwan nan. Ba zai ƙara jawo mutuwa, ko yă hana ƙasar ba da amfani ba.’”
22 Så blev Vandet sundt, efter det Ord Elisa talte; og det er det den Dag i dag.
Ruwan ya tsabtacce har yă zuwa yau, bisa ga faɗin Elisha.
23 Derfra begav han sig op til Betel. Som han var på Vej derop, kom nogle Smådrenge ud af Byen og spottede ham og råbte: "Kom herop, Skaldepande, kom herop, Skaldepande!"
Daga nan sai Elisha ya tafi Betel. Yayinda yake tafiya a hanya, sai waɗansu matasa suka fito daga cikin gari, suka yi masa dariya suna cewa, “Ka haura, ya kai mai kai marar gashi! Ka haura, kai mai kai marar gashi!”
24 Han vendte sig om, og da han fik Øje på dem, forbandede han dem i HERRENs Navn. Så kom to Bjørne ud af Krattet og sønderrev to og fyrretyve af Drengene.
Sai ya juya ya dube su, ya la’anta su da sunan Ubangiji. Sai beyar guda biyu suka fito daga jeji suka hallaka matasa arba’in da biyu daga cikinsu.
25 Derfra begav han sig til Karmels Bjerg, og derfra vendte han tilbage til Samaria.
Sai ya ci gaba zuwa Dutsen Karmel, daga can kuma ya koma Samariya.