< Anden Kongebog 1 >

1 Efter Alkahs Død faldt Moab fra Israel.
Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
2 Og Ahazja faldt ud gennem Vinduesgitteret for sin Stue på Taget i Samaria og blev syg; da sendte han Sendebud af Sted og sagde til dem: "Gå hen og spørg Ekrons Gud Ba'al-Zebub, om jeg kommer mig af min Sygdom!"
Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
3 Men HERRENs Engel sagde til Tisjbiten Elias: "Gå Sendebudene fra Samarias Konge i Møde og sig til dem: Mon det er, fordi der ingen Gud er i Israel, at I drager hen for at rådspørge Ekrons Gud Ba'al-Zebub?
Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
4 Derfor, så siger HERREN: Det Leje, du steg op på, kommer du ikke ned fra, thi du skal dø!" Dermed gik Elias bort.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
5 Da Sendebudene kom tilbage til ham, spurgte han dem: "Hvorfor kommer I tilbage?"
Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
6 De svarede: "En Mand kom os i Møde og sagde til os: Vend tilbage til Kongen, som har sendt eder, og sig: Så siger HERREN: Mon det er, fordi der ingen Gud er i Israel, at du sender Bud for at rådspørge Ekrons Gud Ba'al-Zebub? Derfor: Det Leje, du steg op på, kommer du ikke ned fra, thi du skal dø!"
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
7 Han spurgte dem da: "Hvorledes så den Mand ud, som kom eder i Møde og sagde disse Ord til eder?"
Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
8 De svarede: "Det var en Mand i en lådden Kappe med et Læderbælte om Lænderne." Da sagde han: "Det er Tisjbiten Elias."
Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
9 Derpå sendte han en Halvhundredfører med hans halvtredsindstyve Mand ud efter ham; og da han kom op til ham på Bjergets Top, hvor han sad, sagde han til ham: "Du Guds Mand! Kongen byder: Kom ned!"
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
10 Men Elias svarede Halvhundredføreren: "Er jeg en Guds Mand, så fare Ild ned fra Himmelen og fortære dig og dine halvtredsindstyve Mand!" Da for Ild ned fra Himmelen og fortærede ham og hans halvtredsindstyve Mand.
Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
11 Atter sendte Kongen en Halvhundredfører med hans halvtredsindstyve Mand ud efter ham; og da han kom derop, sagde han til ham: "Du Guds Mand! Således siger Kongen: Kom straks ned!"
Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
12 Men Elias svarede ham: "Er jeg en Guds Mand, så fare Ild ned fra Himmelen og fortære dig og dine halvtredsindstyve Mand!" Da for Guds Ild ned fra Himmelen og fortærede ham og hans halvtredsindstyve Mand.
Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
13 Atter sendte Kongen en Halvhundredfører ud efter ham: men da den tredje Halvhundredfører kom derop, kastede han sig på Knæ for Elias, bønfaldt ham og sagde: "du Guds Mand! Lad dog mit og disse dine halvtredsindstyve Trælles Liv være dyrebarl i dine Øjne!
Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
14 Se, Ild for ned fra Himmelen og fortærede de to første Halvhundredførere og deres halvtredsindstyve Mand, men lad nu mit Liv være dyrebart i dine Øjne!"
Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
15 Da sagde HERRENs Engel til Elias: "Gå ned med ham, frygt ikke for ham!" Så gik han ned med ham og fulgte ham til Kongen.
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
16 Og han sagde til Kongen: "Så siger HERREN: Fordi du har sendt Sendebud hen at rådspørge Ekrons Gud Ba'al-Zebub - men det er, fordi der ingen Gud er i Israel, du kunde rådspørge? - derfor: Det Leje, du steg op på, kommer du ikke ned fra, thi du skal dø!"
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
17 Og han døde efter det HERRENs Ord, som Elias havde talt. Og hans Broder Joram blev Konge i hans Sted i Josafats Søns, Kong Joram af Judas, andet Regeringsår; thi han havde ingen Søn.
Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
18 Hvad der ellers er at fortælle om Ahazja, hvad han udførte, står jo optegnet i Israels Kongers Krønike.
Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?

< Anden Kongebog 1 >