< Anden Krønikebog 5 >

1 Da hele Arbejdet, som Salomo lod udføre ved HERRENs Hus, var færdigt, bragte Salomo sin Fader Davids Helliggaver, Sølvet og Guldet, derind og lagde alle Tingene i Skatkamrene i Guds Hus.
Sa’ad da dukan aikin da Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji ya gama, sai ya kawo abubuwan da mahaifinsa Dawuda ya keɓe a ciki, azurfa da zinariya da kuma dukan kayayyaki, ya kuwa sa su a cikin ma’ajin haikalin Allah.
2 Derpå kaldte Salomo Israels Ældste og alle Stammernes Overhoveder, Israeliternes Fædrenehuses Øverster, sammen i Jerusalem for at føre HERRENs Pagts Ark op fra Davidsbyen, det er Zion.
Sa’an nan Solomon ya tattara zuwa Urushalima dattawan Isra’ila, dukan kawunan kabilu da manyan iyalan Isra’ilawa, don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
3 Så samledes alle Israels Mænd hos Kongen på Højtiden i Etanim Måned, det er den syvende Måned.
Dukan mutanen Isra’ila kuwa suka tattaru gaba ɗaya suka zo wurin sarki a lokacin biki a wata na bakwai.
4 Og alle Israels Ældste kom, og Leviterne har Arken.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin,
5 Og de bragte Arken op tillige med Åbenbaringsteltett og alle de hellige Ting, der var i Teltet; Præsterne og Leviterne bragte dem op:
suka haura da akwatin alkawarin da kuma Tentin Sujada da dukan kayayyaki masu tsarkin da yake cikinta. Firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, suka ɗauke su;
6 Og Kong Salomo tillige med hele Israels Menighed, som havde givet Møde hos ham foran Arken, ofrede Småkvæg og Hornkvæg, så meget, at det ikke var til at tælle eller overse.
Sarki Solomon kuwa da taron Isra’ila gaba ɗaya da suka taru kewaye da shi suna a gaban akwatin alkawarin, suna miƙa tumaki da shanu masu yawa da suka wuce ƙirge ko lissafi.
7 Så førte Præsterne HERRENs Pagts Ark ind på dens Plads i Templets Inderhal, det Allerhelligste, og stillede den under Kerubernes Vinger;
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurinsa a ciki cikin wuri mai tsarki na haikali, Wuri Mafi Tsarki, suka sa shi ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
8 og Keruberne udbredte deres Vinger over Pladsen, hvor Arken stod, og således dannede Keruberne et Dække over Arken og dens Bærestænger.
Kerubobin suka buɗe fikafikansu a bisa wurin akwatin alkawari suka kuma rufe akwatin alkawarin da sandunan ɗaukonsa.
9 Stængerne var så lange, at Enderne af dem kunde ses fra det Hellige foran Inderhallen, men de kunde ikke ses længere ude; og de er der den Dag i Dag.
Waɗannan sanduna sun yi tsawo ƙwarai har ƙarshensu sun nausa daga akwatin alkawarin, ana iya ganinsu daga gaban ciki wuri mai tsarki na can ciki amma ba daga waje Wuri Mai Tsarki ba; kuma suna nan a can har wa yau.
10 Der var ikke andet i Arken end de to Tavler, Moses havde lagt ned i den på Horeb, Tavlerne med den Pagt, HERREN havde sluttet med Israeliterne, da de drog bort fra Ægypten.
Babu wani abu a cikin akwatin alkawarin sai alluna biyu da Musa ya sa a cikinsa a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
11 Da Præsteme derpå gik ud af Helligdommen - alle de Præster, der var til Stede, havde nemlig helliget sig uden Hensyn til Skifterne;
Sa’an nan firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki. Dukan firistocin da suke can sun tsarkake kansu, ko daga wace ɓangarori suka fito.
12 og alle de levitiske Sangere, Asaf, Heman og Jedutun tillige med deres Sønner og Brødre stod østen for Alteret i Klæder af fint Linned med Cymbler, Harper og Citre, og sammen med dem stod 120 Præster, der blæste i Trompeter -
Dukan Lawiyawa waɗanda suke mawaƙa, Asaf, Heman, Yedutun da’ya’yansu maza da dangoginsu, suka tsaya a gefen gabas na bagaden, saye da lilin mai kyau suna kuma kaɗa ganguna, garayu da molaye. Tare da su akwai firistoci 120 masu busan ƙahoni.
13 i samme Øjeblik som Trompetblæserne og Sangerne på een Gang stemte i for at love og prise HERREN og lod Trompeterne, Cymblerne og Musikinstrumenterne klinge og lovede HERREN med Ordene "thi han er god, og hans Miskundhed varer evindelig!" - fyldte Skyen HERRENs Hus,
Masu busan ƙahonin da mawaƙa suka haɗu da baki ɗaya sai ka ce murya guda ce, don su yabi su kuma yi godiya ga Ubangiji. Haɗe da busan ƙahoni, ganguna da sauran kayayyaki, suka tā da muryoyinsu cikin yabo ga Ubangiji suka rera, “Yana da kyau; ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Sai haikalin Ubangiji ya cika da girgije,
14 så at Præsterne af Skyen hindredes i at stå og udføre deres Tjeneste, thi HERRENs Herlighed fyldte Guds Hus.
Firistoci ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalin Allah.

< Anden Krønikebog 5 >