< Anden Krønikebog 33 >
1 Manasse var tolv År gammel, da han blev Konge, og han herskede fem og halvtredsindstyve År i Jerusalem.
Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
2 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENs Øjne, og efterlignede de Folkeslags Vederstyggeligheder, som HERREN havde drevet bort foran Israeliterne.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 Han byggede atter de Offerhøje, som hans Fader Ezekias havde nedrevet, rejste Altre for Ba'alerne, lavede Asjerastøtter og tilbad hele Himmelens Hær og dyrkede dem.
Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
4 Og han byggede Altre i HERRENs Hus, om hvilket HERREN havde sagt: "I Jerusalem skal mit Navn være til evig Tid."
Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
5 Og han byggede Altre for hele Himmelens Hær i begge HERRENs Hus's Forgårde.
Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
6 Han lod sine Sønner gå igennem Ilden i Hinnoms Søns Dal, drev Trolddom og tog Varsler, drev hemmelige Kunster og ansatte Dødemanere og Sandsigere; han gjorde meget, som var ondt i HERRENs Øjne, og krænkede ham.
Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
7 Det Gudebillede, han lod lave, opstillede han i Guds Hus, om hvilket Gud havde sagt til David og hans Søn Salomo: "I dette Hus og i Jerusalem, som jeg har udvalgt af alle Israels Stammer, vil jeg stedfæste mit Navn til evig Tid;
Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 og jeg vil ikke mere fjerne Israels Fod fra det Land, jeg gav deres Fædre, dog kun på det Vilkår, at de omhyggeligt overholder alt, hvad jeg har pålagt dem, hele Loven, Anordningerne og Lovbudene, som de fik ved Moses,"
Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
9 Men Manasse forførte Juda og Jerusalems Indbyggere til at handle værre end de Folkeslag, HERREN havde udryddet for Israeliterne.
Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 Da talede HERREN Manasse og hans Folk til, men de ænsede det ikke.
Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
11 Så førte HERREN Assyrerkongens Hærførere mod dem, og de fangede Manasse med Kroge, lagde ham i Kobberlænker og førte ham til Babel.
Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
12 Men da han var i Nød, bad han HERREN sin Gud om Nåde og ydmygede sig dybt for sine Fædres Gud.
Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
13 Og da han bad til ham, bønhørte han ham; han hørte hans Bøn og bragte ham tilbage til Jerusalem til hans Kongedømme; da indså Manasse, at HERREN er Gud.
Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
14 Senere byggede han en ydre Mur ved Davidsbyen vesten for Gihon i Dalen og hen imod Fiskeporten, så at den omsluttede Ofel; og han byggede den meget høj. I alle de befæstede Byer i Juda ansatte han Hærførere.
Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
15 Han fjernede de fremmede Guder og Gudebilledet fra HERRENs Hus og alle de Altre, han havde bygget på Tempelbjerget og i Jerusalem, og kastede dem uden for Byen.
Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
16 Og han istandsatte HERRENs Alter og ofrede Tak- og Lovprisningsofre derpå; og han bød Juda at dyrke HERREN, Israels Gud.
Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
17 Men Folket vedblev at ofre på Offerhøjene, dog kun til HERREN deres Gutd.
Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
18 Hvad der ellers er at fortælle om Manasse, hans Bøn til sin Gud og de Seeres Ord, som talte til ham i HERRENs, Israels Guds, Navn, står jo optegnet i Israels Kongers Krønike;
Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
19 hans Bøn og Bønhørelse, al hans Synd og Troløshed og de Steder, hvor han opførte Offerhøje og opstillede Asjerastøtter og Gudebilleder, før han ydmygede sig, står jo optegnet i Seernes Krønike.
Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
20 Så lagde Manasse sig til Hvile hos sine Fædre, og man jordede ham i Haven ved hans Hus; og hans Søn Amon blev Konge i hans Sted.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Amon var to og tyve År gammel, da han blev Konge, og han hersltede to År i Jerusalem.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
22 Han gjorde, hvad der var ondt i HERRENs Øjne, ligesom hans Fader Manasse, og Amon ofrede til alle de Gudebilleder, hans Fader Manasse havde ladet lave, og dyrkede dem.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
23 Han ydmygede sig ikke for HERRENs Åsyn, som hans Fader Manasse havde gjort, men Amon dyngede Skyld på Skyld.
Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
24 Hans Tjenere sammensvor sig imod ham og dræbte ham i hans Hus;
Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
25 men Folket fra Landet dræbte alle dem, der havde sammensvoret sig imod Kong Amon, og gjorde hans Søn Josias til Konge i hans Sted.
Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.