< 1 Tessalonikerne 2 >

1 I vide jo selv, Brødre! at vor Indgang hos eder ikke har været forgæves;
Domin ku da kanku kun sani, 'yan'uwa, cewa zuwan mu gareku, ba a banza yake ba.
2 men skønt vi, som I vide, forud havde lidt og vare blevne mishandlede i Filippi, fik vi Frimodighed i vor Gud til at tale Guds Evangelium til eder under megen Kamp.
Kun kuma san yadda aka wulakantar damu, aka kuma kunyatar damu a Filibi, kamar yadda kuka sani. Muna nan kuwa da karfin zuciya cikin Allahnmu domin yi maku bisharar Allah cikin fama da yawa.
3 Thi vor Prædiken skyldes ikke Bedrag, ej heller Urenhed og er ikke forbunden med Svig;
Domin kuwa gargadinmu zuwa a gare ku ba gurbatacciya bace, ko cikin rashin tsarki, ba kuma ta yaudara bace.
4 men ligesom vi af Gud ere fundne værdige til at få Evangeliet betroet, således tale vi, ikke for at behage Mennesker, men Gud, som prøver vore Hjerter.
A maimako, kamar yadda Allah ya amince damu, ya kuma damka mana amanar bishararsa, haka kuma muke yin magana. Muna maganar ba domin mu gamshi mutane ba, amma domin mu gamshi Allah. Domin shi ne yake gwada zuciyarmu.
5 Thi vor Færd var hverken nogen Sinde med smigrende Tale - som I vide - ej heller var den et Skalkeskjul for Havesyge - Gud er Vidne;
Domin bamu taba yi maku dadin baki ba, ko sau daya, kamar yadda kuka sani, ko kwadayi a asirce, kamar yadda Allah shine shaidar mu.
6 ikke heller søgte vi Ære af Mennesker, hverken af eder eller af andre, skønt vi som Kristi Apostle nok kunde have været eder til Byrde.
Bamu kuma nemi daukaka daga mutane ko daga gare ku ko kuma wadansu ba. Da mun so da mun mori ikonmu a matsayin manzannin Almasihu.
7 Men vi færdedes med Mildhed iblandt eder. Som når en Moder ammer sine egne Børn,
A maimakon haka, mun kaskantar da kanmu a tsakanin ku kamar yadda uwa take ta'azantar da 'ya'yan ta.
8 således fandt vi, af inderlig Kærlighed til eder, en Glæde i at dele med eder ikke alene Guds Evangelium, men også vort eget Liv, fordi I vare blevne os elskelige.
Don haka muna da kauna domin ku, ba bisharar Allahnmu kadai muke jin dadin yi maku ba, amma harda bada rayukan mu domin ku. Domin kun zama kaunatattu ne a garemu,
9 I erindre jo, Brødre! vor Møje og Anstrengelse; arbejdende Nat og Dag, for ikke at være nogen af eder til Byrde, prædikede vi Guds Evangelium for eder.
Kufa tuna, 'yan'uwa, game da aikinmu da famarmu. Dare da rana muna aiki sosai domin kada mu nawaita wa kowane dayan ku. A lokacin da muke yi maku bisharar Allah.
10 I ere Vidner, og Gud, hvor fromt og retfærdigt og ulasteligt vi færdedes iblandt eder, som tro;
Ku shaidu ne, haka ma Allah, yadda muka yi rayuwar tsarki da kuma adalci da rashin abin zargi a wajenku wadanda kuka bada gaskiya.
11 ligesom I vide, hvorledes vi formanede og opmuntrede hver enkelt af eder som en Fader sine Børn
Don haka kun kuma sani yadda muka rika yi da kowannenku, kamar uba da 'ya'yansa, yadda muka yi ma ku garadi da kuma karfafa ku, mun kuma shaida.
12 og besvore eder, at I skulde vandre Gud værdigt, ham, som kaldte eder til sit Rige og sin Herlighed.
Domin ku yi tafiya a hanyar da ta dace ga Allah, wanda ya kira ku zuwa ga mulkinsa da kuma daukakarsa.
13 Og derfor takke også vi Gud uafladelig, fordi, da I modtoge Guds Ord, som I hørte af os, toge I ikke imod det som Menneskers Ord, men som Guds Ord (hvad det sandelig er), hvilket også viser sig virksomt i eder, som tro.
Domin wannan dalili ne yasa muke yi wa Allah godiya a koyaushe. Domin a lokacin da kuka karbi maganar Allah daga wurinmu wadda kuka ji, kun karbeta da gaske ba kamar maganar mutum ba. A maimako, kuka karbeta da gaskiyarta, kamar yadda take, maganar Allah. Wannan kalma kuma ita ce ke aiki a cikin ku wadanda kuka yi bangaskiya.
14 Thi I, Brødre! ere blevne Efterfølgere af Guds Menigheder i Judæa i Kristus Jesus, efterdi også I have lidt det samme af eders egne Stammefrænder, som de have lidt af Jøderne,
Domin ku 'yan'uwa, kun zama masu koyi da ikilisiyoyin Allah da ke Yahudiya cikin Almasihu Yesu. Domim kuma kun sha wahala irin tamu daga wurin mutanen kasarku kamar yadda suma suka sha a hannun Yahadawa.
15 der både ihjelsloge den Herre Jesus og Profeterne og udjoge os og ikke behage Gud og stå alle Mennesker imod,
Yahudawane suka kashe Ubangiji Yesu da sauran Annabawa, kuma Yahudawane suka koro mu, Basu gamshi Allah ba. A maimako, suna hamayya da dukkan mutane.
16 idet de forhindre os i at tale til Hedningerne til deres Frelse, for til enhver Tid at fylde deres Synders Mål; men Vreden er kommen over dem fuldtud.
Sun kuma haramta mana yin magana da Al'ummai domin su sami ceto. Sakamakon haka kuwa kullum suna cika zunubansu. Fushi kuma ya afko kansu daga karshe.
17 Men vi, Brødre! som en stakket Tid have været skilte fra eder i det ydre, ikke i Hjertet, vi have gjort os des mere Flid for at få eders Ansigt at se, under megen Længsel,
Mu kuma, 'yan'uwa, mun rabu daku na karamin lokaci, a zahiri, ba a zuciya ba, mun kuma yi iyakar kokarinmu da marmarin ganin fuskarku.
18 efterdi vi have haft i Sinde at komme til eder, jeg, Paulus, både een og to Gange, og Satan har hindret os deri.
Domin mun yi maramarin zuwa gareku. Ni, Bulus, ba sau daya ba, amma Shaidan ya hanamu.
19 Thi hvem er vort Håb eller vor Glæde eller vor Hæderskrans, når ikke også I ere det for vor Herre Jesus Kristus i hans Tilkommelse?
To menene begenmu a gaba, ko murnarmu ko rawanin alfahari, a gaban Ubangijinmu Yesu a ranar zuwansa? Ko ba ku bane, da kuma sauran jama'a?
20 I ere jo vor Ære og Glæde.
Don kuwa kune daukakarmu da kuma farin cikinmu.

< 1 Tessalonikerne 2 >