< 1 Samuel 20 >

1 Men David flygtede fra Najot i Rama og kom til Jonatan og sagde: "Hvad har jeg gjort? Hvad er min Brøde? Og hvad er min Synd mod din Fader, siden han står mig efter Livet?"
Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
2 Han svarede: "Det være langt fra! Du skal ikke dø! Min Fader foretager sig jo intet, hverken stort eller småt, uden at lade mig det vide; hvorfor skulde min Fader så dølge dette for mig? Der er intet om det!"
Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
3 Men David svarede: "Din Fader ved sikkert, at du har fattet Godhed for mig, og tænker så: Det må Jonatan ikke få at vide, at det ikke skal gøre ham ondt; nej, så sandt HERREN lever, og så sandt du lever, der er kun et Skridt imellem mig og Døden!"
Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
4 Da sagde Jonatan til David: "Alt, hvad du ønsker, vil jeg gøre for dig!"
Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
5 David sagde til Jonatan: "I Morgen er det jo Nymånedag, og jeg skulde sidde til Bords med Kongen; men lad mig gå bort og skjule mig på Marken indtil Aften.
Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
6 Hvis din Fader savner mig, så sig: David har bedt mig om Lov til at skynde sig til Betlehem, sin Fødeby, da hele hans Slægt har sit årlige Slagtoffer der.
In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
7 Hvis han så siger: Godt! er der ingen Fare for din Træl; men bliver han vred, så vid, at han vil min Ulykke.
In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
8 Vis din Træl den Godhed, siden du er gået i Pagt med din Træl for HERRENs Åsyn. Men har jeg forbrudt mig, så slå du mig ihjel; thi hvorfor skulde du bringe mig til din Fader?"
Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
9 Jonatan svarede: "Det være langt fra! Hvis jeg virkelig kommer under Vejr med, at min Fader vil din Ulykke, skulde jeg så ikke lade dig det vide?"
Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
10 Da sagde David til Jonatan: "Men hvem skal lade mig det vide, om din Fader giver dig et hårdt Svar?"
Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
11 Jonatan svarede David: "Kom, lad os gå ud på Marken!" Og de gik begge ud på Marken.
Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
12 Da sagde Jonatan til David: "HERREN, Israels Gud, er Vidne: Jeg vil i Morgen ved denne Tid udforske min Faders Sindelag, og hvis der ingen Fare er for David, skulde jeg da ikke sende dig Bud og lade dig det vide?
Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
13 HERREN ramme Jonatan både med det ene og det andet: Hvis det er min Faders bestemte Vilje at bringe Ulykke over dig, vil jeg lade dig det vide og hjælpe dig bort, så du kan fare i Fred. HERREN være med dig, som han har været med min Fader.
Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
14 Og måtte du så, hvis jeg endnu er i Live, måtte du så vise HERRENs Godhed imod mig. Men skulde jeg være død,
Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
15 så unddrag ingen Sinde min Slægt din Godhed. Og når HERREN udrydder hver eneste af Davids Fjender af Jorden,
Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
16 måtte da Jonatans Navn ikke blive udryddet, men bestå sammen med Davids Hus, og måtte HERREN kræve det af Davids Fjenders Hånd!"
Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
17 Da svor Jonatan på ny David en Ed, fordi han elskede ham; thi han elskede ham af hele sin Sjæl.
Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
18 Da sagde Jonatan til ham: "I Morgen er det Nymånedag; da vil du blive savnet, når din Plads står tom;
Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
19 men i Overmorgen vil du blive savnet endnu mere; gå så hen til det Sted, hvor du holdt dig skjult, den Dag Skændselsdåden skulde have fundet Sted, og sæt dig ved Jorddyngen der;
Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
20 i Overmorgen vil jeg så skyde med Pile der, som om jeg skød til Måls.
Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
21 Jeg sender så Drengen hen for at lede efter Pilen, og hvis jeg da siger til ham: Pilen ligger her på denne Side af dig, hent den! så kan du komme; thi da står alt vel til for dig, og der er ingen Fare, så sandt HERREN lever.
Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
22 Men siger jeg til den unge Mand: Pilen ligger på den anden Side af dig, bedre frem! så fly, thi da vil HERREN have dig bort.
Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
23 Men om det, vi to har aftalt sammen, gælder, at HERREN står mellem mig og dig for evigt!"
Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
24 David skjulte sig så ude på Marken. Da Nymånedagen kom, satte Kongen sig til Bords for at spise;
Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
25 Kongen sad på sin vante Plads, på Pladsen ved Væggen, medens Jonatan sad lige overfor og Abner ved Siden af Saul, men Davids Plads stod tom.
Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
26 Saul sagde intet den Dag, thi han tænkte: "Der er vel hændet ham noget, så han ikke er ren, fordi han endnu ikke har renset sig."
Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
27 Men da Davids Plads også stod tom næste Dag, Dagen efter Nymånedagen, sagde Saul til sin Søn Jonatan: "Hvorfor kom Isajs Søn hverken til Måltidet i Går eller i Dag?"
Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
28 Jonatan svarede Saul: "David bad mig om Lov til at gå til Betlehem;
Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
29 han sagde: Lad mig gå, thi vor Slægt har Offerfest der i Byen, og mine Brødre har pålagt mig at komme; hvis du har Godhed for mig, lad mig så få fri, for at jeg kan besøge mine Slægtninge! Det er Grunden til, at han ikke er kommet til Kongens Bord!"
Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
30 Da blussede Sauls Vrede op imod Jonatan, og han sagde til ham; "Du Søn af en vanartet Kvinde! Ved jeg ikke, at du er Ven med Isajs Søn til Skam for dig selv og for din Moders Blusel?
Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
31 Thi så længe Isajs Søn er i Live på Jorden, er hverken du eller dit Kongedømme i Sikkerhed. Send derfor Bud og hent ham til mig, thi han er dødsens!"
Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
32 Jonatan svarede sin Fader Saul: "Hvorfor skal han dræbes? Hvad har han gjort?"
Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
33 Da kastede Saul Spydet efter ham for at ramme ham. Så skønnede Jonatan, at det var hans Faders bestemte Vilje at dræbe David.
Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
34 Og Jonatan rejste sig fra Bordet i heftig Vrede og spiste intet den anden Nymånedag, thi det gjorde ham ondt for David, at hans Fader havde smædet ham.
Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
35 Næste Morgen gik Jonatan fulgt af en dreng ud i Marken, til den Tid han havde aftalt med David.
Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
36 Derpå sagde han til Drengen, han havde med: "Løb hen og led efter den Pil, jeg skyder af!" Medens Drengen løb, skød han Pilen af over hans Hoved,
Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
37 og da Drengen nåede Stedet, hvor Pilen, som Jonatan havde afskudt, lå, råbte Jonatan til ham: "Pilen ligger jo på den anden Side af dig, bedre frem!"
Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
38 Derpå råbte Jonatan til Drengen: "Skynd dig alt, hvad du kan, og bliv ikke stående!" Så tog Jonatans dreng Pilen og bragte sin Herre den.
Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
39 Og Drengen vidste ikke noget, thi kun Jonatan og David kendte Sammenhængen.
(Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
40 Jonatan gav derpå sin Dreng Våbnene og sagde til ham: "Tag dem med til Byen!"
Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
41 Da Drengen var gået, rejste David sig fra sit Skjul ved Jorddyngen og faldt til Jorden på sit Ansigt og bøjede sig ned tre Gange. Og de kyssede hinanden og græd bitterlig sammen.
Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
42 Derpå sagde Jonatan til David: "Far i Fred! Om det, vi to har tilsvoret hinanden i HERRENs Navn, gælder, at HERREN står mellem mig og dig, mellem mine og dine Efterkommere for evigt!" Så brød David op og drog bort, medens Jonatan gik ind i Byen.
Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.

< 1 Samuel 20 >