< 1 Peter 1 >
1 Peter, Jesu Kristi Apostel, til Udlændingene i Adspredelse i Pontus, Galatien, Kappadokien, Asien og Bithynien,
Bitrus, manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga zaɓaɓɓu na Allah, baƙi a duniya, da suke a warwatse ko’ina a Fontus, Galatiya, Kaffadokiya, Asiya da kuma Bitiniya,
2 udvalgte efter Gud Faders Forudviden, ved Åndens Helligelse, til Lydighed og Bestænkelse med Jesu Kristi Blod: Nåde og Fred vorde eder mangfoldig til Del!
waɗanda aka zaɓa bisa ga rigyasanin Allah Uba, ta wurin aikin tsarkakewar Ruhu, don biyayya ga Yesu Kiristi, su kuma sami yayyafan jininsa. Alheri da salama su zama naku a yalwace.
3 Lovet være Gud og vor Herres Jesu Kristi Fader, som efter sin store Barmhjertighed har genfødt os til et levende Håb ved Jesu Kristi Opstandelse fra de døde,
Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi! Cikin jinƙansa mai girma ya ba mu sabuwar haihuwa cikin bege mai rai ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
4 til en uforkrænkelig og ubesmittelig og uvisnelig Arv, som er bevaret i Himlene til eder,
da kuma cikin gādon da ba zai taɓa lalacewa, ɓacewa ko koɗewa ba, ajiyayye a sama dominku,
5 I, som ved Guds Kraft bevogtes ved Tro til en Frelse, som er rede til at åbenbares i den sidste Tid,
ku waɗanda ta wurin bangaskiya ake kiyayewa ta wurin ikon Allah har yă zuwa ceton da yake a shirye da za a bayyana a ƙarshen lokaci.
6 i hvilken I skulle fryde eder, om I end nu en liden Stund, hvis så skal være, bedrøves i mange Hånde Prøvelser,
A kan wannan kuke cike da farin ciki ƙwarai, ko da yake yanzu na ɗan lokaci kuna fuskantar baƙin ciki daga gwaje-gwaje iri-iri.
7 for at eders prøvede Tro, som er meget dyrebarere end det forgængelige Guld, der dog prøves ved Ild, må findes til Ros og Herlighed og Ære i Jesu Kristi Åbenbarelse,
Wannan kuwa domin a tabbatar da sahihancin bangaskiyarku ne, wadda ta fi zinariya daraja nesa, ita zinariya kuwa, ko da yake mai ƙarewa ce, akan gwada ta da wuta, domin bangaskiyan nan taku ta jawo muku yabo da girma da ɗaukaka a bayyanar Yesu Kiristi.
8 ham, som I ikke have set og dog elske, ham, som I, skønt I nu ikke se, men tro, skulle fryde eder over med en uudsigelig og forherliget Glæde,
Ko da yake ba ku taɓa ganinsa ba, kuna ƙaunarsa; kuma ko da yake ba kwa ganinsa yanzu, kun gaskata shi, kun kuma cika da farin ciki ƙwarai, wanda ya fi gaban faɗi,
9 når I nå Målet for eders Tro, Sjælenes Frelse.
gama kuna samun sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku ke nan.
10 Om denne Frelse have Profeter gransket og ransaget, de, som profeterede om den Nåde, der skulde blive eder til Del,
Game da ceton nan, annabawa, waɗanda suka yi maganar alherin da za tă zo gare ku, sun yi bincike mai zurfi, a natse,
11 idet de granskede over, hvilken eller hvordan en Tid Kristi Ånd, som var i dem, henviste til, når den forud vidnede om Kristi Lidelser og den derpå følgende Herlighed.
suna ƙoƙari su san lokaci da kuma yanayin da Ruhun Kiristi da yake cikinsu yana nunawa sa’ad da ya yi faɗi a kan wahalolin Kiristi da kuma ɗaukaka da za tă bi.
12 Og det blev dem åbenbaret, at det ikke var dem selv, men eder, de tjente med disse Ting, som nu ere blevne eder kundgjorte ved dem, der have forkyndt eder Evangeliet i den Helligånd, som blev sendt fra Himmelen, hvilke Ting Engle begære at skue ind i.
Aka bayyana musu cewa ba kansu ne suke bauta wa ba sai ku, sa’ad da suka yi maganar abubuwan da aka faɗa muku ta wurin waɗanda suka yi muku wa’azin bishara, ta wurin Ruhu Mai Tsarki wanda aka aika daga sama. Ko mala’iku ma suna marmari su ga waɗannan abubuwa.
13 Derfor, binder op om eders Sinds Lænder, værer ædrue, og sætter fuldt ud eders Håb til den Nåde, som bliver eder til Del i Jesu Kristi Åbenbarelse.
Saboda haka, ku shirya kanku don aiki; ku zama masu kamunkai; ku kafa begenku duka a kan alherin da za a ba ku sa’ad da aka bayyana Yesu Kiristi.
14 Som lydige Børn skulle I ikke skikke eder efter de forrige Lyster i eders Vankundighed;
Kamar’ya’ya masu biyayya, kada ku bi mugayen sha’awace-sha’awacen da dā kuke da su sa’ad da kuke rayuwa a cikin jahilci.
15 men efter den hellige, som kaldte eder, skulle også I vorde hellige i al eders Vandel;
Amma kamar yadda wanda ya kira ku yake mai tsarki, haka ku ma sai ku kasance masu tsarki cikin dukan abubuwan da kuke yi;
16 thi der er skrevet: "I skulle være hellige, thi jeg er hellig."
gama a rubuce yake cewa, “Ku zama masu tsarki, domin ni mai tsarki ne.”
17 Og dersom I påkalde ham som Fader, der dømmer uden Persons Anseelse efter enhvers Gerning, da bør I vandre i Frygt eders Udlændigheds Tid,
Tun da yake kuna kira ga Uba wanda yake yin wa kowane mutum shari’a bisa ga ayyukansa ba bambanci, sai ku yi rayuwarku a nan kamar baƙi cikin tsoro mai bangirma.
18 vel vidende, at det ikke var med forkrænkelige Ting, Sølv eller Guld, at I bleve løskøbte fra eders tomme Vandel, som var overleveret eder fra Fædrene,
Gama kun san cewa ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa ko zinariya ce aka fanshe ku daga rayuwar banza da kuka karɓa daga kakanni-kakanninku ba,
19 men med Kristi dyrebare Blod som et lydeløst og uplettet Lams,
sai dai an fanshe ku da jini mai daraja na Kiristi, ɗan rago marar aibi ko lahani.
20 han, som var forud kendt for Verdens Grundlæggelse, men blev åbenbaret ved Tidernes Ende for eders Skyld,
An zaɓe shi kafin halittar duniya, amma an bayyana shi a zamanin ƙarshe saboda ku.
21 der ved ham tro på Gud, som oprejste ham fra de døde og gav ham Herlighed, så at eders Tro også er Håb til Gud.
Ta gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya tā da shi daga matattu, aka kuma ɗaukaka shi, ta haka bari bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.
22 Lutrer eders Sjæle i Lydighed imod Sandheden til uskrømtet Broderkærlighed, og elsker hverandre inderligt af Hjertet,
Yanzu da kuka tsarkake kanku ta wurin yin biyayya ga gaskiyan nan, don ku kasance da ƙauna mai gaskiya wa’yan’uwanku, sai ku ƙaunaci juna ƙwarai, daga zuciya.
23 genfødte, som I ere, ikke af forkrænkelig, men af uforkrænkelig Sæd, ved Guds levende og blivende Ord. (aiōn )
Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. (aiōn )
24 Thi "alt Kød er som Græs, og al dets Herlighed som Græssets Blomst; Græsset visner, og Blomsten falder af;
Gama, “Dukan mutane kamar ciyawa suke, darajarsu kuma kamar furannin jeji ne; ciyawa takan yanƙwane furannin kuma su kakkaɓe,
25 men Herrens Ord bliver evindelig." Og dette er det Ord, som er forkyndt eder ved Evangeliet. (aiōn )
amma maganar Ubangiji tana nan har abada.” Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi. (aiōn )