< 1 Peter 4 >
1 Efterdi da Kristus har lidt i Kødet, så skulle også I væbne eder med det samme Sind (thi den, som har lidt i Kødet, er hørt op med Synd),
Saboda haka, da yake Kiristi ya sha wahala a jikinsa, sai ku ma ku yi wa kanku ɗamara da irin wannan hali, gama wanda ya sha wahala a jikinsa ya gama da zunubi ke nan.
2 så at I ikke fremdeles leve den øvrige Tid i Kødet efter Menneskers Lyster, men efter Guds Villie.
Ta haka, ba ya sauran rayuwarsa a kan mugayen sha’awace-sha’awacen jiki, sai dai nufin Allah.
3 Thi det er nok i den forbigangne Tid at have gjort Hedningernes Villie, idet I have vandret i Uterlighed, Lyster, Fylderi, Svir, Drik og skammelig Afgudsdyrkelse;
Gama kun ɓata lokaci sosai a dā kuna yin abubuwan da masu bauta gumaka suka zaɓa su yi, kuna rayuwa cikin lalata, sha’awace-sha’awace, buguwa, shashanci, shaye-shaye da kuma bautar gumaka masu banƙyama.
4 hvorfor de forundre sig og spotte, når I ikke løbe med til den samme Ryggesløshedens Pøl;
Sun yi mamaki da ba kwa haɗa kai da su a yanzu, da ba kwa kutsa kai tare da su cikin irin rayuwar banzan nan, har suna zaginku.
5 men de skulle gøre ham Regnskab, som er rede til at dømme levende og døde.
Amma dole su ba da lissafi gare shi wanda yake a shirye yă shari’anta masu rai da matattu.
6 Thi derfor blev Evangeliet forkyndt også for døde, for at de vel skulde være dømte på Menneskers Vis i Kødet, men leve på Guds Vis i Ånden.
Dalilin ke nan da ya sa aka yi wa’azin bishara har ga waɗanda yanzu suke mutattu, don ko da yake an hukunta su a matsayin mutane a batun jiki, amma su rayu ga Allah a batun ruhu.
7 Men alle Tings Ende er kommen nær; værer derfor årvågne og ædru til Bønner!
Ƙarshen abubuwa duka ya yi kusa. Saboda haka ku kasance masu tunani mai kyau da masu kamunkai don ku iya yin addu’a.
8 Hav fremfor alt en inderlig Kærlighed til hverandre; thi "Kærlighed skjuler en Mangfoldighed af Synder".
Fiye da kome, ku ƙaunaci juna sosai, domin ƙauna tana rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
9 Vær gæstfri imod hverandre uden Knurren.
Ku riƙa karɓar juna ba da gunaguni ba.
10 Eftersom enhver har fået en Nådegave, skulle I tjene hverandre dermed som gode Husholdere over Guds mangfoldige Nåde.
Kowa yă yi amfani da kowace baiwar da ya samu don kyautata wa waɗansu, cikin aminci yana aikata alherin Allah a hanyoyi dabam-dabam.
11 Taler nogen, han tale som Guds Ord; har nogen en Tjeneste, han tjene, efter som Gud forlener ham Styrke dertil, for at Gud må æres i alle Ting ved Jesus Kristus, hvem Herligheden og Magten tilhører i Evighedernes Evigheder! Amen. (aiōn )
In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
12 I elskede! undrer eder ikke over den Ild, som brænder iblandt eder til eders Prøvelse, som om der hændtes eder noget underligt;
Abokaina ƙaunatattu, kada ku yi mamakin gwaji mai tsananin da kuke sha, sai ka ce wani baƙon abu ne yake faruwa da ku.
13 men glæder eder i samme Mål, som I have Del i Kristi Lidelser, for at I også kunne glæde og fryde eder ved hans Herligheds Åbenbarelse.
Sai dai ku yi murna cewa kuna tarayya cikin shan wahalolin Kiristi, domin ku kai ga farin ciki mai yawa sa’ad da aka bayyana ɗaukakarsa.
14 Dersom I hånes for Kristi Navns Skyld, ere I salige; thi Herlighedens og Guds Ånd hviler over eder.
In an zage ku saboda sunan Kiristi, ku masu albarka ne, gama Ruhun ɗaukaka da kuma na Allah yana bisanku.
15 Thi ingen af eder bør lide som Morder eller Tyv eller Ugerningsmand eller som en, der blander sig i anden Mands Sager;
In kuna shan wahala, kada yă zama don ku masu kisankai ne ko ɓarayi ko masu wani irin laifi ko kuma masu shisshigi.
16 men lider han som en Kristen, da skamme han sig ikke, men prise Gud for dette Navn!
Amma fa, in kuka sha wahala a matsayin ku Kirista ne, kada ku ji kunya, sai dai ku yabi Allah cewa kuna amsa wannan suna.
17 Thi det er Tiden til, at Dommen skal begynde med Guds Hus: men begynder den først med os, hvad Ende vil det da få med dem, som ere genstridige imod Guds Evangelium?
Gama lokaci ya yi da za a fara yi wa iyalin Allah shari’a; in kuwa ya fara da mu, to, me zai faru da waɗanda ba sa biyayya da bisharar Allah?
18 Og dersom den retfærdige med Nød og neppe bliver frelst, hvor skal da den ugudelige og Synderen blive af?
Kuma, “In da ƙyar masu adalci su kuɓuta, me zai faru da marasa tsoron Allah da kuma masu zunubi?”
19 Derfor skulle også de, som lide efter Guds Villie, befale den trofaste Skaber deres Sjæle, idet de gøre det gode.
Saboda haka, waɗanda suke shan wahala bisa ga nufin Allah ya kamata su danƙa kansu ga Mahaliccinsu mai aminci, su kuma ci gaba da aikata abin da yake daidai.