< Første Kongebog 3 >
1 Da nu Salomo havde fået Kongedømmet sikkert i hænde besvogrede han sig med Farao, Ægypterkongen, idet han ægtede Faraos Datter; og han førte hende ind i Davidsbyen, til han fik sit eget Hus, HERRENs Hus og Muren om Jerusalem bygget færdig.
Solomon ya haɗa kai da Fir’auna sarkin Masar, ya kuwa auri’yarsa. Ya kawo ta cikin Birnin Dawuda kafin yă gama ginin fadarsa, da haikalin Ubangiji, da kuma katanga kewaye da Urushalima.
2 Kun ofrede Folket på Offerhøjene, thi hidindtil var der ikke bygget HERRENs Navn et Hus.
A lokacin dai mutane suna miƙa hadaya a wurare a bisa tuddai, domin ba a riga an gina haikali saboda Sunan Ubangiji ba.
3 Salomo elskede HERREN, så at han vandrede efter sin Fader Davids Anordninger; kun ofrede han på Højene og tændte Offerild der.
Solomon ya ƙaunaci Ubangiji ta wurin yin tafiya bisa ga farillan mahaifinsa Dawuda, sai dai ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a wuraren nan na bisa tuddai.
4 Og Kongen begav sig til Gibeon for at ofre der; thi det var den store Offerhøj; tusind Brændofre ofrede Salomo på Alteret der.
Sai sarki Solomon ya tafi Gibeyon don yă miƙa hadayu, gama a can ne wuri mafi muhimmanci na sujada. Solomon kuwa ya miƙa hadayun ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade.
5 I Gibeon lod HERREN sig til Syne for Salomo i en Drøm om Natten. Og Gud sagde: "Sig, hvad du ønsker, jeg skal give dig!"
A Gibeyon, Ubangiji ya bayyana ga Solomon da dare a mafarki, Allah ya ce, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.”
6 Da sagde Salomo: "Du viste stor Miskundhed mod din Tjener, min Fader David, der jo også vandrede for dit Åsyn i Troskab, Retfærdighed og Hjertets Oprigtighed; og du lod denne store Miskundhed blive over ham og gav ham en Søn, der nu sidder på hans Trone.
Solomon ya amsa ya ce, “Ka nuna alheri mai girma ga bawanka, mahaifina Dawuda domin ya yi aminci gare ka da adalci, ya kuma kasance da zuciya mai gaskiya. Ka ci gaba da wannan alheri mai girma gare shi, ka ba shi ɗa don yă zauna a kujerar sarautarsa a wannan rana.
7 Ja, nu har du, HERRE min Gud, gjort din Tjener til Konge i min Fader Davids Sted. Men jeg er ganske ung og ved ikke, hvorledes jeg skal færdes ret;
“Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka sa bawanka a wurin mahaifina Dawuda. Amma ni ɗan yaro ne kawai, ban kuma san yadda zan yi ayyukana ba.
8 og din Tjener står midt i det Folk, du udvalgte, et stort Folk, som ikke kan tælles eller udregnes, så mange er de.
Bawanka yana nan a cikin mutanen da ka zaɓa, mutane masu girma, waɗanda suka wuce ƙirge, ko a lissafta.
9 Giv derfor din Tjener et lydhørt Hjerte, så han kan dømme dit Folk og skelne mellem godt og ondt; thi hvem kan dømme dette dit store Folk!"
Saboda haka ka ba bawanka zuciyar ganewa, don yă shugabanci mutanenka, yă kuma iya rarrabe tsakanin abin da yake daidai da abin da ba daidai ba. Gama wa zai iya shugabance wannan mutanenka masu girma haka?”
10 Det vakte HERRENs Velbehag, at Salomo bad derom;
Sai Ubangiji ya ji daɗi cewa Solomon ya roƙa wannan.
11 og Gud sagde til ham: "Fordi du bad om dette og ikke om et langt Liv, ej heller om Rigdom eller om dine Fjenders Liv, men om Forstand til at skønne, hvad ret er,
Saboda haka Allah ya ce masa, “Da yake ka nemi wannan ne, ba ka kuwa nemi tsawon rai ko arziki wa kanka ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, amma ka nemi ganewa a aikata gaskiya,
12 se, derfor vil jeg gøre, som du beder: Se, jeg giver dig et viist og forstandigt Hjerte, så at din Lige aldrig før har været, ej heller siden skal fremstå;
zan yi abin da ka roƙa. Zan ba ka zuciya mai hikima da ta ganewa, har yă zama ba a taɓa samun wani kamar ka ba, ba kuwa za a taɓa samunsa ba.
13 men jeg giver dig også, hvad du ikke bad om, både Rigdom og Ære, så at du ikke skal have din Lige blandt Konger, så længe du lever.
Ban da haka ma, zan ba ka abin da ba ka nema ba; arziki da girma, don a rayuwarka ba za ka kasance da wani kamar ka ba a cikin sarakuna.
14 Og hvis du vandrer på mine Veje, så du holder mine Anordninger og Bud, således som din Fader David gjorde, vil jeg give dig et langt Liv."
In kuma ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi biyayya da farillaina da umarnaina kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, zan ba ka tsawon rai.”
15 Da vågnede Salomo, og se, det var en Drøm. Derpå begav han sig til Jerusalem og stillede sig foran HERRENs Pagts Ark og ofrede Brændofre, bragte Takofre og gjorde et Gæstebud for alle sine Folk.
Sai Solomon ya farka, ya gane ashe mafarki ne. Ya koma Urushalima, ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama. Sa’an nan ya shirya wa fadawansa biki.
16 På den Tid kom to Skøger til Kongen og trådte frem for ham.
To, ana nan sai waɗansu karuwai biyu suka zo wurin sarki, suka tsaya a gabansa.
17 Den ene Kvinde sagde: "Hør mig, Herre! Jeg og den Kvinde der bor i Hus sammen. Hjemme i vort Hus fødte jeg i hendes Nærværelse et Barn,
Sai ɗaya ta ce, “Ranka yă daɗe, wannan mata da ni muna zama a gida ɗaya. Na haifi jariri yayinda take can tare da ni.
18 og tre Dage efter min Nedkomst fødte også hun et Barn. Vi var sammen; der var ingen andre hos os i Huset, vi to var ene i Huset.
Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
19 Så døde hendes Dreng om Natten, fordi hun kom til at ligge på ham;
“Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
20 men midt om Natten, medens din Trælkvinde sov, stod hun op og tog min Dreng fra min Side og lagde ham ved sit Bryst; men sin døde Dreng lagde hun ved mit Bryst.
Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.
21 Da jeg så om Morgenen rejste mig for at give min Dreng at die, se, da var han død; men da jeg så nøje på ham om Morgenen, se, da var det ikke min Dreng, ham, som jeg havde født!"
Kashegari, da na farka don in shayar da ɗana, sai na tarar ya mutu! Amma sa’ad da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ashe ba ɗan da na haifa ba ne.”
22 Men den anden Kvinde sagde: "Det er ikke sandt; den levende er min Dreng, og den døde er din!" Og den første sagde: "Nej, den døde er din Dreng, og den levende er min!" Således mundhuggedes de foran Kongen.
Amma ɗaya matar ta ce, “A’a! Mai rai ɗin ne ɗana; mataccen naki ne.” Amma ta farin ta nace, “A’a! Mataccen ne naki; mai ran ne nawa.” A haka suka yi ta gardama a gaban sarki.
23 Da sagde Kongen: "Den ene siger: Han her, den levende, er min Dreng, den døde er din! Og den anden siger: Nej, den døde er din Dreng, den levende min!"
Sarki ya ce, “Wannan ta ce, ‘Ɗana ne a raye, naki ne matacce,’ yayinda ɗayan tana cewa, ‘A’a! Ɗanki ne mataccen, nawa ne a raye.’”
24 Derpå sagde Kongen: "Hent mig et Sværd!" Og de bragte Kongen et.
Sai sarki ya ce, “Kawo mini takobi.” Sai aka kawo takobi wa sarki.
25 Da sagde Kongen: "Hug det levende Barn over og giv hver af dem det halve!"
Ya ba da umarni ya ce, “Yanka yaron nan mai rai, gida biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
26 Da rørte Kærligheden til Barnet sig heftigt i den Kvinde, som var Moder til det levende Barn, og hun sagde til Kongen: "Hør mig, Herre! Giv hende det levende Barn; dræb det endelig ikke!" Men den anden sagde: "Det skal hverken tilhøre mig eller dig, hug det kun over!"
Ainihin mamar ɗan da yake a raye ta cika da tausayi saboda ɗanta, sai ta ce wa sarki, “Ina roƙonka, ranka yă daɗe, kada ka kashe yaron! Ka ba ta kawai!” Amma ɗayan matar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu ɗan da rai, a ci gaba a raba shi!”
27 Da tog Kongen til Orde og sagde: "Giv hende der det levende Barn og dræb det ikke; thi hun er Moderen!"
Sai sarki ya zartar da hukuncinsa ya ce, “A ba da jariri mai ran ga mata ta fari. Kada a kashe shi; ita ce ainihin mahaifiyarsa.”
28 Og da Israel hørte om den Dom, Kongen havde fældet, fyldtes de alle af Ærefrygt for Kongen; thi de så, at han sad inde med Guds Visdom til at skifte Ret.
Sa’ad da dukan Isra’ila suka ji hukuncin da sarki ya zartar, suka girmama sarki sosai, domin sun gane cewa Allah ya ba shi hikimar yin shari’ar adalci.