< Første Kongebog 18 >
1 Lang Tid efter, i det tredie År, kom HERRENs ord således: "Gå hen og træd frem for Akab, så vil jeg sende Regn over Jorden!"
Bayan dogon lokaci, a cikin shekara ta uku, maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce, “Tafi, ka gabatar da kanka ga Ahab, zan kuwa aika da ruwan sama a ƙasar.”
2 Da gav Elias sig på Vej for at træde frem for Akab. Da Hungersnøden blev trykkende i Samaria,
Saboda haka Iliya ya tafi ya gabatar da kansa ga Ahab. Yanzu dai yunwa ta tsananta a Samariya,
3 kaldte Akab Paladsøversten Obadja til sig. Obadja var en Mand, der alvorligt frygtede HERREN,
Ahab kuma ya aika a kawo Obadiya, sarkin fadansa (Obadiya dai cikakken mai gaskata da Ubangiji ne.
4 og dengang Jesabel lod HERRENs Profeter udrydde, tog han og skjulte hundrede Profeter, halvtredsindstyve i een Hule og halvtredsindstyve i en anden, og sørgede for Brød og Vand til dem.
Yayinda Yezebel tana kisan annabawan Ubangiji, Obadiya ya ɗauki annabawa ɗari ya ɓoye a kogwanni biyu, hamsin a kowanne, ya kuma tanada musu abinci da kuma ruwa.)
5 Akab sagde nu til Obadja: "Kom, lad os drage rundt i Landet til alle Vandkilder og Bække, om vi mulig kan finde så meget Græs, at vi kan holde Liv i Hestene og Muldyrene og slippe for at dræbe noget af Dyrene!"
Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka ratsa ƙasar zuwa dukan maɓulɓulai da fadamu. Mai yiwuwa ka sami ciyawa mu ba dawakai da alfadarai don su rayu, don kada mu kashe dabbobinmu.”
6 Så delte de Landet, som de skulde gennemvandre, mellem sig, således at Akab og Obadja drog hver sin Vej.
Saboda haka suka raba ƙasar da za su ratsa, Ahab zai tafi gefe ɗaya, Obadiya kuma yă bi gefe ɗaya.
7 Medens nu Obadja var undervejs, se, da trådte Elias ham i Møde; Obadja genkendte ham og faldt på sit Ansigt og sagde: "Er det dig, min Herre Elias?"
Yayinda Obadiya yana tafiya, sai Iliya ya sadu da shi. Obadiya ya gane shi, ya rusuna har ƙasa, ya ce, “Kai ne, shugabana, Iliya?”
8 Han svarede: "Ja, det er mig! Gå hen og sig til din Herre, at Elias er her!"
Iliya ya amsa, ya ce, “I, je ka faɗa wa maigidanka cewa, ‘Iliya yana a nan.’”
9 Men han sagde: "Hvormed har jeg dog syndet, siden du vil give din Træl i Akabs Hånd, for at han kan slå mig ihjel?
Obadiya ya yi tambaya, “Me na yi da ba daidai ba, da kake miƙa bawanka ga Ahab don yă kashe?
10 Så sandt HERREN din Gud lever, der er ikke et Folk eller Rige, min Herre ikke har sendt Bud til for at lede efter dig; og blev der sagt, at du ikke var der, tog han Riget og Folket i Ed på, at de ikke havde fundet dig.
Na rantse da Ubangiji Allahnka, babu al’umma ko masarauta da mai girma sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka can, sai yă sa mulkin ko al’ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba.
11 Og nu siger du, at jeg skal gå hen og sige til min Herre, at Elias er her!
Amma yanzu kana faɗa mini in tafi wurin mai girma in ce, ‘Iliya yana a nan.’
12 Hvis nu HERRENs Ånd, når jeg har forladt dig, fører dig bort til et Sted, jeg ikke kender, og jeg kommer og melder det til Akab, og han ikke finder dig, lader han mig dræbe. Og din Træl har dog frygtet HERREN fra Ungdommen af!
Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
13 Er det ikke kommet min Herre for Øre, hvad jeg gjorde, da Jesabel lod HERRENs Profeter dræbe, hvorledes jeg skjulte hundrede af HERRENs Profeter, halvtredsindstyve i een Hule og halvtredsindstyve i en anden, og sørgede for Brød og Vand til dem?
Ranka yă daɗe, ashe, ba a faɗa maka abin da na yi lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji ba? Yadda na ɓoye annabawa ɗari, na sa su hamsin-hamsin a kogwanni biyu, na yi ta ba su abinci da ruwa.
14 Og nu siger du, at jeg skal gå hen og sige til din Herre, at Elias er her - han lader mig dræbe!"
Yanzu fa, kana ce in tafi wurin mai girma sarki, in ce, ‘Iliya yana a nan.’ Ai, zai kashe ni!”
15 Da sagde Elias: "Så sandt Hærskarers HERRE lever, han, for hvis Åsyn jeg står, i Dag vil jeg træde frem for ham."
Iliya ya ce, “Na rantse da Ubangiji Maɗaukaki, wanda nake bauta wa, tabbatacce zan gabatar da kaina ga Ahab a yau.”
16 Obadja gik da Akab i Møde og meldte ham det, og Akab gik Elias i Møde.
Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya.
17 Da Akab fik Øje på Elias, sagde han til ham: "Er det dig, du, som bringer Ulykke over Israel!"
Sa’ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne wannan, kai mai tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila?”
18 Men han svarede: "Det er ikke mig, der har bragt Ulykke over Israel, men dig og din Faders Hus, fordi I har forladt HERREN og holder eder til Ba'alerne!
Iliya ya amsa, ya ce, “Ban tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila ba. Amma kai da iyalin mahaifinka, ku kuka tā-da-na-zaune-tsaye. Ka ƙyale umarnai Ubangiji, ka bi Ba’al.
19 Men send nu Bud og kald hele Israel sammen til mig på Karmels Bjerg og tillige de 450 Ba'alsprofeter og de 400 Asjeraprofeter, som spiser ved Jesabels Bord!"
Yanzu ka tara mutane daga dukan Isra’ila su sadu da ni a kan Dutsen Karmel. Ka kuma kawo annabawa ɗari huɗu da hamsin na Ba’al, da kuma annabawa ɗari huɗu na Ashera, waɗanda suke ci a teburin Yezebel.”
20 Da sendte Akab Bud rundt til alle Israeliterne og samlede Profeterne på Karmels Bjerg.
Sai Ahab ya aika a duk fāɗin Isra’ila, ya kuma tattara annabawan a kan Dutsen Karmel.
21 Elias trådte så frem for alt Folket og sagde: "Hvor længe vil I blive ved at halte til begge Sider? Er HERREN Gud, så hold eder til ham, og er Ba'al Gud, så hold eder til ham!" Men Folket svarede ham ikke et Ord.
Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
22 Da sagde Elias til Folket: "Jeg er den eneste af HERRENs Profeter, der er tilbage, og Ba'als Profeter er 450 Mand;
Sai Iliya ya ce musu, “Ni ne kaɗai annabin Ubangiji da ya rage, amma Ba’al yana da annabawa ɗari huɗu da hamsin.
23 lad os nu få to unge Tyre; så skal de vælge den ene Tyr og hugge den i Stykker og lægge den på Brændet, men Ild må de ikke lægge til; den anden vil jeg lave til og lægge på Brændet, men uden at tænde Ild.
Ku samo mana bijimai biyu. Bari su zaɓa ɗaya wa kansu, bari kuma su yanka shi kucu-kucu su sa a itace, sai dai, kada su sa wuta a kansa. Ni kuwa zan shirya ɗaya bijimin in sa a kan itace, ni ma, ba zan sa wuta a kansa ba.
24 Så skal I påkalde eders Guds Navn, og jeg vil påkalde HERRENs Navn; den Gud, der svarer med Ild, han er Gud!" Alt Folket sagde: "Det Forslag er godt!"
Sa’an nan ku kira bisa sunan allahnku, ni kuwa zan kira bisa sunan Ubangiji. Duk allahn da ya amsa ta wurin wuta, shi ne Allah.” Sai dukan jama’a suka ce, “Abin nan da faɗa yana da kyau.”
25 Derpå sagde Elias til Ba'als Profefer: "Vælg eder den ene Tyr og lav den til først, thi I er de mange, og påkald så eders Guds Navn, men I må ikke tænde Ild!"
Iliya ya ce wa annabawan Ba’al, “Ku ku fara zaɓi bijimi ɗaya, ku shirya, da yake kuna da yawa. Ku kira a bisa sunan allahnku, amma kada ku ƙuna wuta.”
26 Så tog de Tyren og lavede den til og påkaldte Ba'als Navn fra Morgen til Middag, idet de råbte: "Hør os, Ba'al!" Men ikke en Lyd hørtes, der var ingen, som svarede; og de dansede haltende omkring det Alter, de havde opført.
Sai suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi. Sa’an nan suka kira bisa sunan Ba’al daga safe har tsakar rana. Suna ihu, “Ya Ba’al, ka amsa mana!” Amma babu wata amsa, babu wani da ya amsa. Suka yi ta rawa kewaye da bagaden da suka yi.
27 Men da det var blevet Middag, hånede Elias dem og sagde: "I må råbe højt, thi han er jo en Gud! Han er vel faldet i Tanker eller gået afsides eller rejst bort, eller han er faldet i Søvn og må først vågne!"
Da tsakar rana, Iliya ya fara yin musu ba’a. Ya ce, “Ku yi ihu da ƙarfi, tabbatacce shi allah ne! Mai yiwuwa yana cikin zurfin tunani, ko dai aiki ya yi masa yawa, ko ya yi tafiya. Mai yiwuwa yana barci ne, dole a tashe shi.”
28 Da råbte de højt, og som de havde for Skik, sårede de deres Legemer med Sværd og Spyd, til Blodet flød ned ad dem.
Sai suka yi ta ihu da ƙarfi suna tsattsaga kansu da takuba da māsu, yadda al’adarsu take, sai da jininsu ya yi ta zuba.
29 Og da det var over Middag, begyndte de at rase, og det varede lige til hen imod Afgrødeofferets Tid, men ikke en Lyd hørtes, ingen svarede, og ingen agtede derpå.
Tsakar rana ta wuce, suka ci gaba da ƙoƙari, suna annabci har lokacin miƙa hadayar yamma ya yi. Amma babu wani da ya tanƙa, babu wani da ya amsa, babu wanda ya kula.
30 Da sagde Elias til alt Folket: "Kom hen til mig!" Og da alt Folket var kommet hen til ham, satte han HERRENs nedbrudte Alter i Stand.
Sa’an nan Iliya ya ce wa dukan mutane, “Ku zo nan wurina.” Suka zo wurinsa, ya kuma shirya bagaden Ubangiji, da ya riga ya zama kufai.
31 Elias tog tolv Sten, svarende til Tallet på Jakobs Sønners Stammer, han, til hvem HERRENs Ord lød: "Israel skal dit Navn!"
Iliya ya ɗauki duwatsu goma sha biyu, ɗaya don kowace kabila zuriyar Yaƙub, wanda maganar Ubangiji ta zo masa, cewa, “Sunanka zai zama Isra’ila.”
32 Og af disse Sten byggede han et Alter i HERRENs Navn og gravede rundt om Alteret en Rende på omtrent to Sea Land.
Da waɗannan duwatsun ya gina bagade cikin sunan Ubangiji, ya kuma haƙa wuriya kewaye da shi, isashe da zai ci garwa biyu na irin ƙwayar gyada.
33 Derpå lagde han Brændet tilrette, huggede Tyren i Stykker og lagde den på Brændet.
Ya shirya itace, ya yayyanka bijimin kucu-kucu, ya shimfiɗa shi a itacen. Sa’an nan ya ce musu, “Ku cika manyan tuluna da ruwa, ku zuba a kan hadayar da kuma a kan itacen.” Suka zuba.
34 Så sagde han: "Fyld fire Krukker med Vand og hæld det ud over Brændofferet og Brændet!" Og da de havde gjort det, sagde han: "Een Gang til!" Og da de havde gjort det anden Gang, sagde han: "Een Gang til!" Og de gjorde det endnu en Gang.
Ya ce, “Ku sāke yin haka,” sai suka sāke yin haka. Ya umarta, “Ku yi haka sau na uku,” suka kuma yi haka sau na uku.
35 Det drev af Vand rundt om Alteret, også Renden fik han fyldt med Vand.
Ruwan ya gangara kewaye da bagaden har ma ya cika wuriyar.
36 Men ved Afgrødeofferets Tid trådte Profeten Elias frem og sagde: "HERRE, Abrahams, Isaks og Israels Gud! Lad det kendes i Dag, at dut er Gud i Israel og jeg din Tjener, og at jeg har gjort alt dette på dit Ord!
A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
37 Hør mig, HERRE, hør mig, for at dette Folk må kende, at du HERRE er Gud, og at du atter drager deres Hjerte til dig"
Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, saboda waɗannan mutane su san cewa kai, ya Ubangiji, kai ne Allah, su kuma san cewa kana sāke juye zukatansu zuwa gare ka.”
38 Da for HERRENs Ild ned og fortærede Brændofferet og Brændet og Stenene og Jorden; endog Vandet i Renden slikkede den bort.
Sai wutar Ubangiji ya fāɗo, ya cinye hadayar, itacen, duwatsun da kuma ƙasar, ya lashe ruwan da yake cikin wuriyar.
39 Da alt Folket så det, faldt de på deres Ansigt og råbte: "HERREN er Gud, HERREN er Gud!"
Sa’ad da mutane suka ga wannan, sai suka rusuna, suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji, shi ne Allah! Ubangiji, shi ne Allah!”
40 Men Elias sagde til dem: "Grib Ba'als Profeter, lad ingen af dem slippe bort!" Og de greb dem, og Elias førte dem ned til Kisjonbækken og dræbte dem der.
Sa’an nan Iliya ya umarce su, ya ce, “Ku kama annabawan Ba’al, kada ku bar waninsu yă tsere!” Suka kama su, Iliya kuwa ya sa aka gangara da su zuwa Kwarin Kishon, aka yayyanka su a can.
41 Derpå sagde Elias til Akab: "Gå op og spis og drik, thi der høres Susen af Regn."
Sai Iliya ya ce wa Ahab, “Ka haura gida, ka ci, ka sha, gama ina jin motsin ruwan sama mai yawa.”
42 Da gik Akab op for at spise og drikke; men Elias gik op på Karmels Top og bøjede sig til Jorden med Ansigtet mellem Knæene.
Sai Ahab ya ruga don yă ci, yă sha, amma Iliya ya hau kan ƙwanƙolin Karmel, ya rusuna ƙasa, ya sa fuska a tsakanin gwiwarsa.
43 Så sagde han til sin Tjener: "Gå op og se ud over Havet!" Og han gik op og så ud, men sagde: "Der er intet!" Syv Gange sagde han til ham: "Gå derop igen!" Og syv Gange vendte Tjeneren tilbage.
Ya ce wa bawansa, “Tafi ka dubi wajen teku.” Sai bawan ya haura ya duba. Ya ce, “Ba kome a can.” Sau bakwai Iliya ya ce, “Koma.”
44 Men syvende Gang sagde han: "Nu stiger der en lille Sky op af Havet, så stor som en Mands Hånd!" Da sagde Elias: "Gå hen og sig til Akab: Spænd for og kør hjem, at du ikke skal blive opholdt af Regnen!"
Sau na bakwai, bawan ya ce, “Wani girgije ƙarami kamar hannun mutum yana tasowa daga teku.” Sai Iliya ya ce, “Je ka faɗa wa Ahab, ‘Shirya keken yaƙinka, ka gangara kafin ruwan sama yă tare ka.’”
45 Et Øjeblik efter var Himmelen sort af Stormskyer, og der faldt en voldsom Regn. Akab steg til Vogns og kørte til Jizre'el;
Ana cikin haka, sarari ya ƙara duhunta da girgije, iska ta taso, sai ruwan sama kamar da bakin kwarya ya sauko, Ahab kuwa ya hau zuwa Yezireyel.
46 men HERRENs Hånd kom over Elias, så han omgjordede sine Lænder og løb foran Akab lige til Jizre'el.
Ikon Ubangiji ya sauko a kan Iliya, ya sha ɗamara, ya ruga a guje a gaban Ahab har zuwa Yezireyel.