< 1 Korinterne 5 >

1 I det hele taget høres der om Utugt iblandt eder, og det sådan Utugt, som end ikke findes iblandt Hedningerne, at en lever med sin Faders Hustru.
Ana ba da labari cewa ana lalata a cikinku, irin da ba a ma samu a cikin masu bautar gumaka. Har mutum yana kwana da matar mahaifinsa.
2 Og I ere opblæste og bleve ikke snarere bedrøvede, for at den, som har gjort denne Gerning, måtte udstødes af eders Midte!
Har ya zama muku abin taƙama! Ashe, bai kamata ku cika da baƙin ciki ku kuma daina zumunci da mutumin da yake aikata wannan ba?
3 Thi jeg for min Del, fraværende med Legemet, men nærværende med Ånden, har allerede, som om jeg var nærværende, fældet den Dom over ham, som på sådan, Vis har bedrevet dette,
Ko da yake ba na nan tare da ku cikin jiki, ina tare da ku a cikin ruhu. Na riga na yanke wa wanda ya aikata wannan hukunci, kamar dai ina tare da ku.
4 at, når i vor Herres Jesu Navn I og min Ånd ere forsamlede, så med vor Herres Jesu Kraft
Saboda haka sa’ad da kun taru ikon Ubangijinmu Yesu kuma yana nan, ni ma ina tare da ku.
5 at overgive den pågældende til Satan til Kødets Undergang, for af Ånden kan frelses på den Herres Jesu dag.
Ku miƙa irin wannan mutum ga Shaiɗan, don a hallaka halin nan na mutuntaka, ruhunsa kuma yă sami ceto a ranar da Ubangiji zai dawo.
6 Det er ikke noget smukt, I rose eder af! Vide I ikke, at en liden Surdejg syrer hele Dejgen?
Ku daina taƙama. Ba ku san cewa ɗan ƙanƙanin yisti ne yakan sa dukan curin burodi yă kumbura ba?
7 Udrenser den gamle Surdejg, for at I kunne være en ny Dejg, ligesom I jo ere usyrede; thi også vort Påskelam er slagtet, nemlig Kristus.
Ku kawar da tsohon yisti don ku zama kamar sabon curi da aka yi babu yisti yadda dai kuke. Gama an miƙa Kiristi Ɗan Ragon Bikin Ƙetarewarmu.
8 Derfor, lader os holde Højtid, ikke med gammel Surdejg, ej heller med Sletheds og Ondskabs Surdejg, men med Renheds og Sandheds usyrede Brød.
Saboda haka, sai mu kiyaye Bikin ba da burodi mai tsohon yisti ba, ba kuma da yisti na ƙeta da mugunta ba, sai dai da burodi marar yisti na sahihanci da na gaskiya.
9 Jeg skrev eder til i mit Brev, at I ikke skulle have Samkvem med utugtige,
Na rubuta muku cikin wasiƙata, kada ku yi haɗa kai da masu aikin lalata.
10 ikke i al Almindelighed denne Verdens utugtige eller havesyge og Røvere eller Afgudsdyrkere; ellers måtte I jo gå ud af Verden.
Ko kusa, ba na nufin fasikai marasa bi, ko makwaɗaita da mazambata, ko matsafa, don in haka ne, sai yă zama dole ku fita daga duniya.
11 Men nu skrev jeg til eder, at I ikke skulle have Samkvem, om nogen, der har Navn af Broder, er en utugtig eller en havesyg eller en Afgudsdyrker eller en Skændegæst eller en Dranker eller en Røver, ja, end ikke spise sammen med en sådan.
Yanzu dai ina rubuta muku cewa kada ku haɗa kai da duk mai kiran kansa ɗan’uwa, amma yana fasikanci, ko kwaɗayi, ko bautar gumaka, ko ɓata suna, ko mashayi, ko mazambaci. Kada ku ko ci abinci da irin wannan mutum.
12 Thi hvad kommer det mig ved at dømme dem, som ere udenfor? Dømme I ikke dem, som ere indenfor?
Me zai kai yin hukunci ga waɗanda ba’yan ikkilisiya ba. Ai, waɗanda suke’yan ikkilisiya ne za ku hukunta.
13 Men dem udenfor skal Gud dømme. Bortskaffer den onde fra eder selv!
Allah zai hukunta waɗanda ba namu ba. “Ku yi waje da irin mugun mutumin nan daga cikinku.”

< 1 Korinterne 5 >