< 1 Korinterne 15 >

1 Men jeg kundgør eder, Brødre, det Evangelium, som jeg Forkyndte eder, hvilket I også modtoge, i hvilket I også stå,
Yanzu ina tunashshe ku 'yan'uwa, game da bisharar nan da nake shelarwa, wadda kuka karba kuke kuma dogara da ita.
2 ved hvilket I også frelses, hvis I fastholde, med hvilket Ord jeg forkyndte eder det - ellers troede I forgæves.
Da wannan bishara aka yi maku ceto, idan kuka rike wa'azi da na yi maku da karfi, sai in dama kun gaskanta a banza.
3 Jeg overleverede eder nemlig som noget af det første, hvad jeg også har modtaget: at Kristus døde for vore Synder, efter Skrifterne;
Domin na baku muhimmin sako kamar na farko da na karba: cewa Almasihu ya mutu domin zunubanmu, bisa ga nassosi,
4 og at han blev begravet; og at han er bleven oprejst den tredje Dag, efter Skrifterne;
cewa kuma an bizne shi, ya kuwa tashi daga matattu a rana ta uku bisa ga nassosi.
5 og at han blev set af Kefas, derefter af de tolv;
Cewa kuma ya bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun.
6 derefter blev han set af over fem Hundrede Brødre på een Gang, af hvilke de fleste endnu ere i Live, men nogle ere hensovede;
Daga nan ya bayyana ga 'yan'uwa sama da dari biyar a lokaci guda. Wadanda mafi yawan su na da rai har yau, amma wasun su sun yi barci.
7 derefter blev han set af Jakob, dernæst af alle Apostlene;
Daga nan ya bayyana ga Yakubu, da kuma ga manzannin duka.
8 men sidst af alle blev han set også af mig som det ufuldbårne Foster;
A karshe, sai ya bayyana a gare ni, kamar dan da aka haifa bakwaini.
9 thi jeg er den ringeste af Apostlene, jeg, som ikke er værd at kaldes Apostel, fordi jeg har forfulgt Guds Menighed.
Gama ni ne mafi kankanta a cikin manzanni. Ban cancanci a kira ni manzo ba, domin na tsanantawa ikklisiyar Allah.
10 Men af Guds Nåde er jeg det, jeg er, og hans Nåde imod mig har ikke været forgæves; men jeg har arbejdet mere end de alle, dog ikke jeg, men Guds Nåde, som er med mig.
Amma saboda alherin Ubangiji ina matsayin da nake a yau, kuma alherin sa da ke ciki na ba a banza yake ba. A maimako, nayi aiki tukuru fiye da su duka. Amma duk da haka ba ni bane, amma alherin Allah da ke tare da ni.
11 Hvad enten det da er mig eller de andre, således prædike vi, og således troede I.
Saboda haka ko nine ko Su, haka mukayi wa'azin, haka kuma kuka gaskata.
12 Men når der prædikes, at Kristus er oprejst fra de døde, hvorledes sige da nogle iblandt eder, at der ikke er dødes Opstandelse?
To idan anyi shela a matsayin cewa Yesu ya tashi daga matattu, tayaya wadansunku su ke cewa babu tashin matattu?
13 Dersom der ikke er dødes Opstandelse, da er ikke heller Kristus oprejst.
Amma idan babu tashin matattu, Almasihu ma ai ba a tashe shi ba kenan.
14 Men er Kristus ikke oprejst, da er vor Prædiken jo tom, og eders Tro også tom.
idan kuwa ba a tashi Almasihu ba, wa'azin mu ya zama banza kenan, haka kuma bangaskiyar ku ta zama banza.
15 Men vi blive da også fundne som falske Vidner om Gud, fordi vi have vidnet imod Gud, at han oprejste Kristus, hvem han ikke har oprejst, såfremt døde virkelig ikke oprejses.
Mun kuma zama shaidun karya game Allah kenan, muna shaida akan Allah cewa ya tashi Almasihu daga matattu alhali ko bai tashe shi ba.
16 Thi dersom døde ikke oprejses, da er Kristus ikke heller oprejst.
Domin idan babu tashin matattu, kai, ko Almasihu ma ba a tashe shi ba kenan.
17 Men dersom Kristus ikke er oprejst, da er eders Tro forgæves; så ere I endnu i eders Synder;
Idan har ba a tashi Almasihu ba, bangaskiyar ku a banza take, har yanzu kuma, kuna cikin zunuban ku.
18 da gik altså også de, som ere hensovede i Kristus, fortabt.
To wadanda suka mutu cikin Almasihu kuma sun hallaka kenan,
19 Have vi alene i dette Liv sat vort Håb til Kristus, da ere vi de ynkværdigste af alle Mennesker.
idan a wannan rayuwa ce kadai muke da bege cikin Almasihu, to cikin dukkan mutane munfi kowa zama abin tausayi.
20 Men nu er Kristus oprejst fra de døde, som Førstegrøde af de hensovede.
Amma yanzu, Almasihu ya tashi daga matattu, wanda ya sa shi ya zama nunar fari cikin tashi daga matattu.
21 Thi efterdi Død kom ved et Menneske, er også dødes Opstandelse kommen ved et Menneske.
Domin yadda mutuwa ta shigo duniya ta hanyar mutum guda, hakkan nan ma tashi daga matattu.
22 Thi ligesom alle dø i Adam, således skulle også alle levendegøres i Kristus.
Gama kamar yadda a cikin Adamu duka suka mutu, haka kuma a cikin Almasihu za a rayar da duka.
23 Dog hver i sit Hold: som Førstegrøde Kristus, dernæst de, som tilhøre Kristus, ved hans Tilkommelse.
Amma kowanne da tsarinsa: Almasihu, nunan fari, sannan su wadanda ke na Almasihu za a rayar da su lokacin zuwansa.
24 Derpå kommer Enden, når han overgiver Gud og Faderen Riget, når han har tilintetgjort hver Magt og hver Myndighed og Kraft.
Sa'an nan karshen zai gabato, lokacin da Almasihu zai mika mulkin ga Allah Uba. sa'an nan ne zaya kawar da dukkan mulki, martaba da iko.
25 Thi han bør være Konge, indtil han får lagt alle Fjenderne under sine Fødder.
Gama mulkinsa zai habaka har sai ya sa dukkan makiyansa a karkashin sawayen sa.
26 Den sidste Fjende, som tilintetgøres, er Døden.
Mutuwa kuwa, ita ce makiyi na karshe da za'a hallaka.
27 Han har jo "lagt alle Ting under hans Fødder." Men når han" siger: "Alt er underlagt" - åbenbart med Undtagelse af den, som underlagde ham alt -
Domin “yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” Amma da aka ce” yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” a sarari yake cewa wannan baya hada da wanda yasa dukan komai a karkashin ikonsa ba.
28 når da alle Ting ere blevne ham underlagte, da skal også Sønnen selv underlægge sig ham, som har underlagt ham alle Ting, for at Gud kan være alt i alle.
Idan dukan abu na karkashin mulkinsa, to Dan da kansa zaya kasance a karkashin ikon shi wanda yasa komai a karkashin ikonsa. Wannan zaya kasance ne saboda Allah Uba ya zama dukkan komai cikin dukkan komai.
29 Hvad ville ellers de udrette, som lade sig døbe for de døde? Dersom døde overhovedet ikke oprejses, hvorfor lade de sig da døbe for dem?
ko kuma me zai faru da wadanda ake yi wa baftisma domin matattu? Idan kuwa babu tashin matattu sam sam, ina amfanin yi masu baftisma domin su?
30 Hvorfor udsætte da også vi os hver Time for Fare?
Kuma me yasa muke cikin hadari kowace sa'a?
31 Jeg dør daglig, så sandt jeg har eder, Brødre, at rose mig af i Kristus Jesus, vor Herre.
Ina mutuwa kullum. Wannan nake furtawa ta wurin fahariya, 'yan'uwa, wadda nake da ita cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.
32 Hvis jeg som et almindeligt Menneske har kæmpet med vilde Dyr i Efesus, hvad Gavn har jeg så deraf? Dersom døde ikke oprejses, da "lader os spise og drikke, thi i Morgen dø vi."
Menene ribata, a idanun mutane, idan nayi kokowa da bisashe a Afisa, idan babu tashin matattu? “bari mu ci mu sha, domin gobe zamu mutu.”
33 Farer ikke vild; slet Omgang fordærver gode Sæder!
Kada fa a yaudare ku, domin “tarayya da mugaye takan bata halayen kirki.”
34 Vorder ædrue, som det bør sig, og synder ikke; thi nogle kende ikke Gud; til Skam for eder siger jeg det.
“Ku natsu! kuyi zaman adalci! kada ku cigaba da zunubi. Domin wasunku basu da sanin Allah. Ina fadar wannan domin in baku kunya.
35 Men man vil sige: "Hvorledes oprejses de døde? hvad Slags Legeme komme de med?"
Amma wani zaya ce, “Yaya za'a yi tashin matattu? Wane irin jiki kuma zasu tashi da shi?
36 Du Dåre! det, som du sår, bliver ikke levendegjort, dersom det ikke dør.
Ku jahilai ne sosai! Abinda ka shuka ba zaya fara girma ba sai ya mutu.
37 Og hvad du end sår, da sår du ikke det Legeme, der skal vorde, men et nøgent Korn, være sig af Hvede eller af anden Art.
Abinda ka shuka ba jikin da zaya kasance bane, amma kwayar irin ne kawai. Wanda zaya zama alkama ko wani abu daban.
38 Men Gud giver det et Legeme, således som han har villet, og hver Sædart sit eget Legeme.
Amma Allah zaya bashi jiki yadda ya zaba, ga kowane kwayar iri da nashi jikin.
39 Ikke alt Kød er det samme Kød, men eet er Menneskers, et andet Kvægs Kød, et andet Fugles Kød, et andet Fisks.
Ba duka jiki ne yake iri daya ba. A maimako, akwai jiki irin na mutane, akwai kuma wani irin na dabbobi, kuma wani jikin irin na tsuntsaye, kuma da irin na kifi.
40 Og der er himmelske Legemer og jordiske Legemer; men een er de himmelskes Herlighed, en anden de jordiskes.
Akwai kuma jikina na samaniya da jikina na duniya. Amma daukakar jikin samaniya wata daban ce kuma daukakar jikin duniya daban ce.
41 Een er Solens Glans og en anden Månens Glans og en anden Stjernernes Glans; thi den ene Stjerne er forskellig fra den anden i Glans.
Akwai daukaka irin ta rana, da kuma wata daukakar irin ta wata, da kuma wata daukakar irin ta taurari. Domin wani tauraron ya bambanta da wani wajen daukaka.
42 Således er det også med de dødes Opstandelse: det såes i Forkrænkelighed, det oprejses i Uforkrænkelighed;
Haka yake a tashin matattu. Abinda aka shuka mai lalacewa ne, wanda aka tayar marar lalacewa ne.
43 det såes i Vanære, det oprejses i Herlighed; det såes i Skrøbelighed, det oprejses i Kraft;
An shuka shi cikin rashin daraja; an tayar da shi cikin daukaka. An shuka shi cikin rauni; an tayar da shi cikin iko.
44 der såes et sjæleligt Legeme, der oprejses et åndeligt Legeme. Når der gives et sjæleligt Legeme, gives der også et åndeligt.
An shuka shi jiki na zahiri; an tayar da shi jiki na ruhaniya. Idan akwai jiki na zahiri, to akwai jiki na ruhaniya.
45 Således er der også skrevet: "Det første Menneske, Adam, blev til en levende Sjæl;"den sidste Adam blev til en levendegørende Ånd.
Haka kuma aka rubuta, “Adamu na farko ya zama rayayyen taliki.” Adamu na karshe ya zama Ruhu mai bayar da rai.
46 Men det åndelige er ikke det første, men det sjælelige; derefter det åndelige.
Amma na ruhaniyar ba shine ya fara zuwa ba amma na zahirin, daga nan na ruhaniyar.
47 Det første Menneske var af Jord, jordisk; det andet Menneske er fra Himmelen.
Mutumin farkon ai daga turbaya ya fito, wato na duniya. Amma shi na biyun daga sama yake.
48 Sådan som den jordiske var, sådanne ere også de jordiske; og sådan som den himmelske er, sådanne ere også de himmelske.
kamar yadda mutumin ya fito daga turbaya haka ma wadanda aka halitta da turbaya. kamar yadda mutumin yake daga sama haka ma wadanda ke na sama.
49 Og ligesom vi have båret den jordiskes Billede, således skulle vi også bære den himmelskes Billede!
Kamar yadda muke dauke da jiki mai kamannin turbaya, haka ma zamu kasance da kamannin mutumin sama.
50 Men dette siger jeg, Brødre! at Kød og Blod kan ikke arve Guds Rige, ej heller arver Forkrænkeligheden Uforkrænkeligheden.
To wannan na fada, 'yan'uwa, cewa nama da jini ba za su gaji mulkin Allah ba. Haka kuma mai lalacewa ba za ya gaji marar lalacewa ba.
51 Se, jeg siger eder en Hemmelighed: Alle skulle vi ikke hensove, men vi skulle alle forvandles
Duba! ina gaya maku asirtacciyar gaskiya: Ba dukanmu zamu mutu ba, amma dukanmu za a canza mu.
52 i et Nu, i et Øjeblik, ved den sidste Basun; thi Basunen skal lyde, og de døde skulle oprejses uforkrænkelige, og vi skulle forvandles.
Za a canza mu nan da nan, cikin keftawar ido, a kaho na karshe. Domin za a busa kaho, kuma za a tada matattu marasa lalacewa, kuma za a canza mu.
53 Thi dette forkrænkelige må iføre sig Uforkrænkelighed, og dette dødelige iføre sig Udødelighed.
Domin wannan jiki mai lalacewa dole ya sanya jiki marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa dole ya sanya marar mutuwa.
54 Men når dette forkrænkelige har iført sig Uforkrænkelighed, og dette dødelige har iført sig Udødelighed, da skal det Ord opfyldes, som er skrevet: "Døden er opslugt til Sejr."
Amma idan wannan jiki mai lalacewa ya sanya marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa ya sanya marar mutuwa, sai abinda aka rubuta ya cika, “An hadiye mutuwa cikin nasara.”
55 "Død, hvor er din Sejr? Død, hvor er din Brod?" (Hadēs g86)
“Mutuwa, ina nasararki? Mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs g86)
56 Men Dødens Brod er Synden, og Syndens Kraft er Loven.
Gama dafin mutuwa zunubi ne, kuma ikon zunubi shari'a ce.
57 Men Gud ske Tak, som giver os Sejren ved vor Herre Jesus Kristus!
Amma godiya ga Allah, wanda ya bamu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu!
58 Derfor, mine elskede Brødre! bliver faste, urokkelige, altid rige i Herrens Gerning, vidende, at eders Arbejde er ikke forgæves i Herren.
Saboda haka, ya ku 'yan'uwana kaunatattu, ku dage kuma kada ku jijjigu. Ko yaushe ku habaka da aikin Ubangiji, domin kun san cewa aikinku cikin Ubangiji ba a banza yake ba.

< 1 Korinterne 15 >