< Første Krønikebog 29 >

1 Fremdeles sagde Kong David til hele Forsamlingen: "Min Søn Salomo, som Gud har udvalgt, er ung og uudviklet, og Arbejdet er stort, thi Borgen er ikke bestemt for et Menneske, men for Gud HERREN.
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
2 Jeg har derfor sat al min Kraft ind på til min Guds Hus at tilvejebringe Guldet, Sølvet, Kobberet, Jernet og Træet til det, der skal laves af Guld, Sølv, Kobber, Jern og Træ, desuden Sjohamsten og Indfatningssten, Rubiner, brogede Sten, alle Slags Ædelsten og Marmorsten i Mængde.
Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
3 I min Glæde over min Guds Hus giver jeg der hos til min Guds Hus, hvad jeg ejer af Guld og Sølv, ud over alt, hvad jeg har bragt til Veje til det hellige Hus:
Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
4 3.000 Talenter Guld, Offrguld, og 7.000 Talenter lutret Sølv til at overtrække Bygningernes Vægge med,
talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
5 Guldet til det, der skal forgyldes, og Sølvet til det, der skal forsølves, og til ethvert Arbejde, der skal udføres af Håndværkernes Hånd. Hvem er nu villig til i Dag at bringe HERREN Gaver?"
don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
6 Da kom Øversterne for Fædrenehusene, Øversterne for Israels Stammer, Tusind- og Hundredførerne og Øversterne i Kongens Tjeneste frivilligt
Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
7 og gav til Arbejdet på Guds Hus 5.000 Talenter og 10.000 Darejker Guld, 10.000 Talenter Sølv, 18.000 Talenter Kobber og 100.000 Talenter Jern;
Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
8 og de, som ejede Ædelsten, gav dem til HERRENs Hus's Skat, der stod under Gersoniten Jehiels Tilsyn.
Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
9 Og Folket glædede sig over deres Vilje til at give, thi af et helt Hjerte gav de HERREN frivillige Gaver; også Kong David følte stor Glæde.
Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
10 Og David priste HERREN i hele forsamlingens Nærværelse, og David sagde: "Lovet være du HERRE, vor Fader Israels Gud fra Evighed til Evighed!
Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
11 Din, HERRE, er Storheden, Magten, Æren, Glansen og Herligheden, thi alt i Himmelen og på Jorden er dit; dit, o HERRE, er Riget, og selv løfter du dig som Hoved over alle.
Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
12 Rigdom og Ære kommer fra dig, og du hersker over alt; i din Hånd er Kraft og Vælde, og i din Hånd står det at gøre, hvem det skal være, stor og stærk.
Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
13 Derfor priser vi dig nu, vor Gud, og lovsynger dit herlige Navn!
Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
14 Thi hvad er jeg, og hvad er mit Folk, at vi selv skulde evne at give sådanne frivillige Gaver? Fra dig kommer det alt sammen, og af din egen Hånd har vi givet dig det.
“Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
15 Thi vi er fremmede for dit Åsyn og Gæster som alle vore Fædre; som em Skygge er vore Dage på Jorden, uden Håb!
Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
16 HERRE vor Gud, al denne Rigdom, som vi har bragt til Veje for at bygge dit hellige Navn et Hus, fra din Hånd kommer den, og dig tilhører det alt sammen.
Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
17 Jeg ved, min Gud. at du prøver Hjerter og har Behag i Oprigtighed; af oprigtigt Hjerte har jeg villigt givet alt dette, og nu har jeg set med Glæde, at dit Folk, der er her til Stede, villigt har givet dig Gaver.
Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
18 HERRE, vore Fædre Abrahams, Isaks og Israels Gud, bevar til evig Tid et sådant Sind og sådanne Tanker i dit Folks Hjerte og vend deres Hjerter til dig!
Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
19 Og giv min Søn Salomo et helt Hjerte til at holde dine Bud, Vidnesbyrd og Anordninger og udføre det alt sammen og bygge den Borg, jeg har truffet Forberedelser til at opføre!"
Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
20 Derpå sagde David til hele Forsamlingen: "Lov HERREN eders Gud!" Og hele Forsamlingen lovede HERREN, deres Fædres Gud, og kastede sig ned for HERREN og Kongen.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
21 Så ofrede de Slagtofre til HERREN, og Dagen efter bragte de ham som Brændoffer 1000 Tyre, 1000 Vædre og 1000 Lam med tilhørende Drikofre og en Mængde Slagtofre for hele Israel;
Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
22 og de spiste og drak den Dag for HERRENs Åsyn med stor Glæde. Derefter indsatte de på ny Davids Søn til Konge, og de hyldede ham som HERRENs Fyrste og Zadok som Præst;
Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
23 og Salomo satte sig på HERRENs Trone som Konge i sin Fader Davids Sted; Lykken var med ham, og hele Israel var ham lydigt;
Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
24 og alle Øversterne og Kærnetropperne, ligeledes alle Kong Davids Sønner hyldede Kong Salomo.
Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
25 HERREN gjorde Salomo overmåde mægtig for hele Israels Øjne og gav ham en kongelig Herlighed, som ingen Konge før ham havde haft i Israel.
Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
26 David, Isajs Søn, havde hersket over hele Israel.
Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
27 Tiden, han var Konge over Israel, udgjorde fyrretyve År; i Hebron herskede han syv År, i Jerusalem tre og tredive År.
Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
28 Han døde i en god Alder, mæt af Dage, Rigdom og Ære; og hans Søn Salomo blev Konge i hans Sted.
Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Kong Davids Historie fra først til sidst står optegnet i Seeren Samuels Krønike, Profeten Natans Krønike og Seeren Gads Krønike
Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
30 tillige med hele hans Regering og hans Heltegerninger og de Tildragelser, som hændtes ham og Israel og alle Lande og Riger.
tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.

< Første Krønikebog 29 >