< Første Krønikebog 13 >

1 Efter at have rådført sig med Tusindførerne og Hundredeførerne, alle Øversterne,
Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
2 sagde David til hele Israels Forsamling: "Hvis det tykkes eder godt, og det er HERREN vor Guds Vilje, lad os så sende Bud til vore Brødre, der er tilbage i alle Israels Landsdele, og ligeledes til Præsterne og Leviterne i Byerne, hvor de har deres Græsmarker, at de skal samles hos os,
Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
3 for at vi kan bringe vor Guds Ark tilbage til os, thi i Sauls Dage spurgte vi ikke om den."
Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
4 Og hele Forsamlingen svarede, at det skulde man gøre, thi alt Folket fandt Forslaget rigtigt.
Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
5 Så samlede David bele Israel lige fra Sjihor i Ægypten til Egnen ved Hamat for at hente Guds Ark i Kirjat-Jearim.
Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
6 Derpå drog David og hele tsrael op til Ba'ala, til Kirjat-Jearim i Juda for der at hente Gud HERRENs Ark, over hvilken hans Navn er nævnet, han, som troner over Keruberne.
Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
7 De førte da Guds Ark bort fra Abinadabs Hus på en ny Vogn, og Uzza og Ajo kørte Vognen.
Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
8 David og hele Israel legede af alle Kræfter for Guds Åsyn til Sang og til Citre, Harper, Pauker, Cymbler og Trompeter.
Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
9 Men da de kom til Kidons Tærskeplads, rakte Uzza Hånden ud for at gribe fat i Arken, fordi Okserne snublede.
Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
10 Da blussede HERRENs Vrede op mod Uzza, og han slog ham, fordi han rakte Hånden ud mod Arken, og han døde på Stedet for Guds Åsyn.
Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
11 Men David græmmede sig over, at HERREN havde tilføjet Uzza et Brud. Derfor kaldte man Stedet Perez-Uzza, som det hedder den Dag i Dag.
Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
12 Og David grebes den Dag af Frygt for Gud og sagde: "Hvor kan jeg da lade Guds Ark komme hen hos mig!"
Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
13 Og David flyttede ikke Arken hen hos sig i Davidsbyen, men lod den sætte ind i Gatiten Obed-Edoms Hus.
Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
14 Guds Ark blev så i Obed-Edoms Hus tre Måneder, og HERREN velsignede Obed-Edoms Hus og alt, hvad hans var.
Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.

< Første Krønikebog 13 >