< Zakarias 14 >
1 Se, en Dag kommer, HERRENS Dag, da dit Bytte skal deles i dig.
Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
2 Da samler jeg alle Folkene til Angreb paa Jerusalem; Byen indtages, Husene plyndres, Kvinderne skændes, og Halvdelen af Byens Indbyggere vandrer i Landflygtighed; men Resten af Folket skal ikke udryddes af Byen.
Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
3 Og HERREN drager ud og strider mod disse Folk, som han fordum stred paa Kampens Dag.
Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
4 Paa hin Dag staar hans Fødder paa Oliebjerget østen for Jerusalem, og Oliebjerget skal revne midt over fra Øst til Vest og danne en vældig Dal, idet Bjergets ene Halvdel viger mod Nord, den anden mod Syd.
A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
5 I skal flygte til mine Bjerges Dal, thi Bjergdalen naar til Azal. I skal fly, som I flyede for Jordskælvet i Kong Uzzija af Judas Dage. Og HERREN min Gud kommer og alle de Hellige med ham.
Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
6 Paa hin Dag skal der ikke være Hede eller Kulde og Frost.
A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
7 Det skal være een eneste Dag — HERREN kender den — ikke Dag og Nat; det skal være lyst ved Aftentide.
Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
8 Paa hin Dag skal rindende Vand vælde frem fra Jerusalem; det halve løber ud i Havet mod Øst, det halve i Havet mod Vest, og det baade Sommer og Vinter.
A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
9 Og HERREN skal være Konge over hele Jorden. Paa hin Dag skal HERREN være een og hans Navn eet.
Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
10 Og hele Landet bliver en Slette fra Geba til Rimmon i Sydlandet; men Jerusalem skal ligge højt paa sit gamle Sted. Fra Benjaminsporten til den gamle Ports Sted, til Hjørneporten, og fra Hanan'eltaarnet til de kongelige Vinperser skal det være beboet.
Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
11 Der skal ikke mere lægges Band derpaa, og Jerusalem skal ligge trygt.
Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
12 Men dette skal være den Plage, HERREN lader ramme alle de Folkeslag, som drager i Leding mod Jerusalem: han lader Kødet raadne paa dem i levende Live, Øjnene raadner i deres Øjenhuler og Tungen i deres Mund.
Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
13 Paa hin Dag skal en vældig HERRENS Rædsel opstaa iblandt dem, saa de griber fat i og løfter Haand mod hverandre.
A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
14 Ogsaa Juda skal stride i Jerusalem. Og alle Folkenes Rigdom skal samles trindt om fra, Guld, Sølv og Klæder i saare store Maader.
Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
15 Og samme Plage skal ramme Heste, Muldyr, Kameler, Æsler og alt Kvæg i Lejrene der.
Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
16 Men alle de, der bliver tilbage af alle Folkene, som kommer imod Jerusalem, skal Aar efter Aar drage derop for at tilbede Kongen, Hærskarers HERRE, og fejre Løvhyttefest.
Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
17 Og dersom nogen af Jordens Slægter ikke drager op til Jerusalem for at tilbede Kongen, Hærskarers HERRE, skal der ikke falde Regn hos dem.
In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
18 Og dersom Ægyptens Slægt ikke drager derop og kommer derhen, saa skal de rammes af den Plage, HERREN lader ramme Folkene.
In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
19 Det er Straffen over Ægypterne og alle de Folk, som ikke drager op for at fejre Løvhyttefest.
Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
20 Paa hin Dag skal der staa paa Hestenes Bjælder »Helliget HERREN«. Og Gryderne i HERRENS Hus skal være som Offerskaalene for Alteret;
A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
21 hver Gryde i Jerusalem og Juda skal være helliget Hærskarers HERRE, saa alle de ofrende kan komme og tage af dem og koge deri. Og paa hin Dag skal der ikke mere være nogen Kana'anæer i Hærskarers HERRES Hus.
Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.