< Rut 2 >

1 No'omi havde en Slægtning paa sin Mands Side, en formuende Mand af Elimeleks Slægt ved Navn Boaz.
To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
2 En Dag sagde Moabiterinden Rut til No'omi: »Jeg vil gaa ud i Marken og sanke Aks efter den, for hvis Øjne jeg finder Naade.« Hun svarede hende: »Ja, gør det, min Datter!«
Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
3 Saa gik hun hen og sankede Aks paa Marken efter Høstfolkene; og det traf sig, at Marken tilhørte Boaz, som var af Elimeleks Slægt.
Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
4 Boaz kom just gaaende fra Betlehem; han sagde da til Høstfolkene: »HERREN være med eder!« Og de svarede: »HERREN velsigne dig!«
Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
5 Derpaa sagde Boaz til den Karl, som havde Opsyn med Høstfolkene: »Hvor hører denne unge Kvinde hjemme?«
Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
6 Karlen, som havde Opsyn med Høstfolkene, svarede: »Det er en moabitisk Pige; det er hende, som fulgte med No'omi tilbage fra Moab;
Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
7 hun sagde: Lad mig faa Lov at sanke og samle Aks blandt Negene efter Høstfolkene! Saa kom hun og har holdt ud lige fra i Morges tidlig til nu uden at unde sig et Øjebliks Hvile.«
Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
8 Da sagde Boaz til Rut: »Hør, min Datter! Du skal ikke gaa hen og sanke Aks paa nogen anden Mark! Nej, gaa ikke herfra, men hold dig til mine Piger her;
Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
9 hold Øje med, hvor de høster paa Marken, og gaa bag efter. Jeg har paalagt Karlene, at de ikke maa fortrædige dig; og bliver du tørstig, kan du gaa hen til Karrene og drikke af det, Karlene øser op!«
Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
10 Da faldt hun paa sit Ansigt, bøjede sig til Jorden og sagde til ham: »Hvorledes har jeg fundet Naade for dine Øjne, saa du viser mig Velvilje, skønt jeg er fremmed?«
Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
11 Boaz svarede hende: »Man har fortalt mig alt, hvad du har været for din Svigermoder efter din Mands Død, hvorledes du forlod din Fader og din Moder og dit Fædreland for at drage til et Folk, du ikke tidligere kendte;
Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
12 HERREN gengælde dig, hvad du har gjort, og din Løn blive rigelig fra HERREN, Israels Gud, under hvis Vinger du kom og søgte Ly!«
Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
13 Hun sagde: »Saa har jeg da fundet Naade for dine Øjne, Herre, siden du har trøstet mig og talt venligt til din Trælkvinde, skønt jeg ikke er saa meget som en af dine Trælkvinder!«
Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
14 Ved Spisetid sagde Boaz til hende: »Kom herhen og spis med og dyp din Bid i Eddiken!« Saa satte hun sig hos Høstfolkene, og han rakte hende saa meget ristet Korn, at hun kunde spise sig mæt og endda levne.
A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
15 Da hun rejste sig for at sanke Aks, bød Boaz sine Karle: »Lad hende ogsaa sanke mellem Negene og fornærm hende ikke;
Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
16 I kan ogsaa trække nogle Aks ud af Knipperne til hende og lade dem ligge, saa hun kan sanke dem op, og I maa ikke skænde paa hende!«
Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
17 Saa sankede hun Aks paa Marken lige til Aften; og da hun tærskede, hvad hun havde sanket, var det omtrent en Efa Byg.
Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
18 Derpaa tog hun det og gik til Byen, og hendes Svigermoder saa, hvad hun havde sanket; og Rut tog og gav hende, hvad hun havde levnet efter at have spist sig mæt.
Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
19 Da sagde hendes Svigermoder til hende: »Hvor har du sanket Aks i Dag, hvor har du været? Velsignet være han, der viste dig Velvilje!« Saa fortalte hun sin Svigermoder, hvem hun havde været hos, og sagde: »Den Mand, jeg var hos i Dag, hedder Boaz!«
Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
20 Da sagde No'omi til sin Sønnekone: »HERREN, som ikke har unddraget de levende og døde sin Miskundhed, velsigne ham!« Og No'omi sagde fremdeles til hende: »Den Mand er en nær Slægtning af os; han er en af vore Løsere.«
Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
21 Moabiterinden Rut sagde: »Han sagde ogsaa til mig: Hold dig kun til mine Folk, indtil de er helt færdige med min Høst!«
Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
22 Da sagde No'omi til sin Sønnekone: »Du gør ret, min Datter, i at følge med hans Piger, at man ikke skal volde dig Men paa en anden Mark!«
Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
23 Saa holdt hun sig til Boaz's Piger og sankede Aks der, indtil Byghøsten og Hvedehøsten var til Ende; og hun blev boende hos sin Svigermoder.
Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.

< Rut 2 >